< Zabura 18 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
in finem puero Domini David quae locutus est Domino verba cantici huius in die qua eripuit eum Dominus de manu omnium inimicorum eius et de manu Saul et dixit diligam te Domine fortitudo mea
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Dominus firmamentum meum et refugium meum et liberator meus Deus meus adiutor meus et sperabo in eum protector meus et cornu salutis meae et susceptor meus
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
laudans invocabo Dominum et ab inimicis meis salvus ero
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
circumdederunt me dolores mortis et torrentes iniquitatis conturbaverunt me
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
dolores inferni circumdederunt me praeoccupaverunt me laquei mortis (Sheol h7585)
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
cum tribularer invocavi Dominum et ad Deum meum clamavi exaudivit de templo sancto suo vocem meam et clamor meus in conspectu eius introibit in aures eius
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
et commota est et contremuit terra et fundamenta montium conturbata sunt et commota sunt quoniam iratus est eis
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
ascendit fumus in ira eius et ignis a facie eius exarsit carbones succensi sunt ab eo
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
inclinavit caelos et descendit et caligo sub pedibus eius
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
et ascendit super cherubin et volavit volavit super pinnas ventorum
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
et posuit tenebras latibulum suum in circuitu eius tabernaculum eius tenebrosa aqua in nubibus aeris
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
prae fulgore in conspectu eius nubes eius; transierunt grando et carbones ignis
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
et intonuit de caelo Dominus et Altissimus dedit vocem suam grando et carbones ignis;
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
et misit sagittas et dissipavit eos et fulgora multiplicavit et conturbavit eos
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
et apparuerunt fontes aquarum et revelata sunt fundamenta orbis terrarum ab increpatione tua Domine ab inspiratione spiritus irae tuae
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
misit de summo et accepit me adsumpsit me de aquis multis
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
eripiet me de inimicis meis fortissimis et ab his qui oderunt me quoniam confirmati sunt super me
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
praevenerunt me in die adflictionis meae et factus est Dominus protector meus
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
et eduxit me in latitudinem salvum me faciet quoniam voluit me
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
et retribuet mihi Dominus secundum iustitiam meam et secundum puritatem manuum mearum retribuet mihi
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
quia custodivi vias Domini nec impie gessi a Deo meo
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
quoniam omnia iudicia eius in conspectu meo sunt et iustitias eius non reppuli a me
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
et ero inmaculatus cum eo et observabo ab iniquitate mea
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
et retribuet mihi Dominus secundum iustitiam meam et secundum puritatem manuum mearum in conspectu oculorum eius
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
cum sancto sanctus eris et cum viro innocente innocens eris
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
et cum electo electus eris et cum perverso perverteris
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
quoniam tu populum humilem salvum facies et oculos superborum humiliabis
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
quoniam tu inluminas lucernam meam Domine Deus meus inluminas tenebras meas
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
quoniam in te eripiar a temptatione et in Deo meo transgrediar murum
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Deus meus inpolluta via eius eloquia Domini igne examinata protector est omnium sperantium in eum
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
quoniam quis deus praeter Dominum et quis deus praeter Deum nostrum
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Deus qui praecingit me virtute et posuit inmaculatam viam meam
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
qui perfecit pedes meos tamquam cervorum et super excelsa statuens me
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
qui doces manus meas in proelium et posuisti arcum aereum brachia mea
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
et dedisti mihi protectionem salutis tuae et dextera tua suscepit me et disciplina tua correxit me in finem et disciplina tua ipsa me docebit
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
dilatasti gressus meos subtus me et non sunt infirmata vestigia mea
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
persequar inimicos meos et conprehendam illos et non convertar donec deficiant
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
confringam illos nec poterunt stare cadent subtus pedes meos
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
et praecinxisti me virtute ad bellum subplantasti insurgentes in me subtus me
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
et inimicos meos dedisti mihi dorsum et odientes me disperdisti
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
clamaverunt nec erat qui salvos faceret ad Dominum nec exaudivit eos
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
et comminuam illos ut pulverem ante faciem venti ut lutum platearum delebo eos
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
eripe me de contradictionibus populi constitues me in caput gentium
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
populus quem non cognovi servivit mihi in auditu auris oboedivit mihi
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
filii alieni mentiti sunt mihi filii alieni inveterati sunt et claudicaverunt a semitis suis
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
vivit Dominus et benedictus Deus meus et exaltetur Deus salutis meae
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
Deus qui dat vindictas mihi et subdidit populos sub me liberator meus de gentibus iracundis
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
et ab insurgentibus in me exaltabis me a viro iniquo eripies me
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
propterea confitebor tibi in nationibus Domine et psalmum dicam nomini tuo
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
magnificans salutes regis eius et faciens misericordiam christo suo David et semini eius usque in saeculum

< Zabura 18 >