< Zabura 18 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Au chef des chantres. Par le serviteur de l’Eternel, David, qui prononça en l’honneur du Seigneur les paroles de ce cantique, lorsque l’Eternel l’eut délivré de la main de tous ses ennemis et de la main de Saül. Il dit: Je t’aime, ô Eternel, qui es ma force!
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Seigneur, tu es mon rocher et ma forteresse, un libérateur pour moi; mon Dieu tutélaire en qui je m’abrite, mon bouclier, mon puissant sauveur, mon rempart!
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Gloire, m’écrié-je, à l’Eternel, et je suis délivré de mes ennemis!
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Déjà m’enveloppaient les liens de la mort, les torrents de la perdition me faisaient frémir;
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
j’étais enlacé dans les réseaux de la tombe, surpris dans les filets de la mort. (Sheol )
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
Dans ma détresse, j’invoque le Seigneur, je fais appel à mon Dieu; de son sanctuaire il entend ma voix, mon cri est monté à ses oreilles.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Soudain la terre oscille et tremble, les fondements des montagnes sont ébranlés, secoués par la colère de Dieu.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Des vapeurs s’exhalent, signe de son courroux; de sa bouche sort un feu dévorant, jaillissent de brûlantes étincelles.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Il incline les cieux et descend; sous ses pieds une brume épaisse.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Porté sur les chérubins, il vole, il plane sur les ailes du vent.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Des ténèbres il se fait une mystérieuse retraite, il s’enveloppe, comme d’un pavillon, des eaux obscures, d’opaques nuages.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
De l’éclat qui l’entoure s’élancent ses nuées, la grêle et des flammes ardentes.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
Il tonne dans les cieux, l’Eternel, le Dieu suprême fait entendre sa voix, la grêle et les flammes ardentes.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Il décoche ses flèches et il les disperse, il lance des éclairs et les frappe de stupeur.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Le lit des fleuves s’est découvert, les fondements de la terre ont été mis à nu, à ta voix impérieuse, ô Eternel, au souffle du vent de ta colère.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
Il étend d’en haut sa main, me saisit, me retire du sein des grandes eaux;
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
il me délivre de mon puissant ennemi, de mes adversaires trop forts pour moi.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Ils étaient à l’affût de mes malheurs, mais l’Eternel a été mon appui.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Il m’a mis au large, m’a sauvé parce qu’il m’aime.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
Le Seigneur me traite selon ma droiture, il récompense la pureté de mes mains.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
C’Est que je suis fidèle aux voies du Seigneur, jamais je n’ai trahi mon Dieu.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
Toutes ses lois me sont présentes, ses statuts, je ne m’en écarte point.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
Attaché à lui sans réserve, je me suis tenu en garde contre mes fautes.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Oui, le Seigneur m’a rémunéré selon ma droiture, selon la pureté de mes mains, dont ses yeux sont témoins.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Tu te montres aimant pour qui t’aime, loyal envers l’homme loyal,
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
sincère avec les cœurs purs, mais artificieux avec les pervers!
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Oui, tu viens en aide à un peuple humilié, et tu abaisses les yeux hautains.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Oui, tu fais briller ma lumière! L’Eternel, mon Dieu, illumine mes ténèbres.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
Soutenu par lui, j’attaque un bataillon; grâce à mon Dieu, j’escalade un rempart.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Dieu puissant! parfaite est sa voie; la parole du Seigneur est infaillible, il est le bouclier de quiconque espère en lui.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Qui est Dieu, hormis l’Eternel? Qui un rocher tutélaire, si ce n’est notre Dieu?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Ce Dieu me ceint de force, et me fait suivre une voie parfaite.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Il rend mes pieds agiles comme ceux des biches, et m’installe sur mes hauteurs.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Il instruit mes mains aux combats, mes bras à manier l’arc d’airain.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Tu me prêtes le bouclier de ton secours, ta droite est mon appui, ta bienveillance fait ma supériorité.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Tu donnes de l’aisance à mes pas, et empêches mes talons de chanceler.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Je poursuis mes ennemis, je les atteins; point de relâche que je ne les aie détruits.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Je les abats, ils ne pourront plus se relever, ils gisent désormais à mes pieds.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
C’Est toi qui m’as armé de vaillance pour la guerre, qui fais plier sous moi mes agresseurs;
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
mes ennemis, tu les fais fuir devant moi, et mes adversaires, j’en fais justice.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Ils s’adressent, à bout de ressources, à l’Eternel…: point de réponse!
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Je les écrase comme la poussière qu’emporte le vent, comme la fange des rues, je les pulvérise.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Tu me fais triompher des factions du peuple, tu me places à la tête des nations; des peuplades inconnues deviennent mes tributaires.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
Au seul bruit de mon nom, ils se soumettent à moi, les fils d’un sol étranger me rendent hommage.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Les fils de l’étranger perdent courage, ils tremblent au fond de leurs retraites.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Vivant est le Seigneur, et béni mon rocher! Glorifié le Dieu qui me protège!
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
O Dieu, c’est toi qui me procures vengeance, qui fais tomber des peuples à mes pieds;
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
qui m’arraches à mes ennemis, me fais triompher de mes agresseurs, et échapper aux hommes de violence.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Je te rends donc grâce, Seigneur, à la face des peuples, et je chante ta gloire,
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
ô toi qui assures de grandes victoires à ton roi, qui combles de bienfaits ton oint David et sa postérité à jamais!