< Zabura 17 >

1 Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
Davut'un duası Haklı davamı dinle, ya RAB, Feryadımı işit! Hilesiz dudaklardan çıkan duama kulak ver!
2 Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
Haklı çıkar beni, Çünkü sen gerçeği görürsün.
3 Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
Yüreğimi yokladın, Gece denedin, Sınadın beni, Kötü bir şey bulmadın; Kararlıyım, ağzımdan kötü söz çıkmaz,
4 Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
Başkalarının yaptıklarına gelince, Ben senin sözlerine uyarak Şiddet yollarından kaçındım.
5 Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
Sıkı adımlarla senin yollarını tuttum, Kaymadı ayaklarım.
6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
Sana yakarıyorum, ey Tanrı, Çünkü beni yanıtlarsın; Kulak ver bana, dinle söylediklerimi!
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
Göster harika sevgini, Ey sana sığınanları saldırganlardan sağ eliyle kurtaran!
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
Koru beni gözbebeği gibi; Kanatlarının gölgesine gizle
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
Kötülerin saldırısından, Çevremi saran ölümcül düşmanlarımdan.
10 Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
Yürekleri yağ bağlamış, Ağızları büyük laflar ediyor.
11 Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
İzimi buldular, üzerime geliyorlar, Yere vurmak için gözetliyorlar.
12 Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
Tıpkı parçalamak için sabırsızlanan bir aslan, Pusuya yatan genç bir aslan gibi.
13 Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
Kalk, ya RAB, kes önlerini, eğ başlarını! Kılıcınla kurtar canımı kötülerden,
14 Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
Elinle bu insanlardan, ya RAB, Yaşam payı bu dünyada olan insanlardan. Varsın karınları vereceğin cezalara doysun, Çocukları da yiyip doysun, Artanı torunlarına kalsın!
15 Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.
Ama ben doğruluk sayesinde yüzünü göreceğim senin, Uyanınca suretini görmeye doyacağım.

< Zabura 17 >