< Zabura 148 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji daga sammai, yabe shi a bisa sammai.
Louvae ao Senhor. Louvae ao Senhor desde os céus, louvae-o nas alturas.
2 Yabe shi, dukanku mala’ikunsa, yabe shi, dukanku rundunarsa na sama.
Louvae-o, todos os seus anjos; louvae-o todos os seus exercitos.
3 Yabe shi, rana da wata, yabe shi, dukanku taurari masu haskakawa.
Louvae-o, sol e lua; louvae-o, todas as estrellas luzentes.
4 Yabe shi, ku bisa sammai da kuma ku ruwan bisa sarari.
Louvae-o, céus dos céus, e as aguas que estão sobre os céus.
5 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama ya umarta aka kuwa halicce su.
Louvem o nome do Senhor, pois mandou, e logo foram creados.
6 Ya sa su a wurarensu har abada abadin; ya ba da umarnin da ba zai taɓa shuɗe ba.
E os confirmou para sempre, e lhes deu uma lei que não ultra-passarão.
7 Yabi Ubangiji daga duniya, ku manyan halittun teku da kuma dukan zurfafan teku,
Louvae ao Senhor desde a terra: vós, baleias, e todos os abysmos,
8 walƙiya da ƙanƙara, dusar ƙanƙara da gizagizai, hadirin iskar da suke biyayya da umarnansa,
Fogo e saraiva, neve e vapores, e vento tempestuoso que executa a sua palavra:
9 ku duwatsu da dukan tuddai, itatuwa masu’ya’ya da dukan al’ul,
Montes e todos os outeiros, arvores fructiferas e todos os cedros:
10 namun jeji da dukan dabbobin gida, ƙanana halittu da tsuntsaye masu firiya,
As feras e todos os gados, reptis e aves voadoras:
11 sarakunan duniya da dukan al’ummai, ku sarakuna da dukan masu mulkin duniya,
Reis da terra e todos os povos, principes e todos os juizes da terra:
12 samari da’yan mata, tsofaffi da yara.
Mancebos e donzellas, velhos e creanças,
13 Bari su yabi sunan Ubangiji, gama sunansa ne kaɗai mafi ɗaukaka; darajarsa ta fi ƙarfin duniya da sammai.
Louvem o nome do Senhor, pois só o seu nome é exaltado: a sua gloria está sobre a terra e o céu.
14 Ya tayar wa mutanensa ƙaho, yabon dukan tsarkakansa, na Isra’ila, mutanen da suke kurkusa da zuciyarsa. Yabi Ubangiji.
Elle tambem exalta o poder do seu povo, o louvor de todos os seus sanctos, dos filhos de Israel, um povo que lhe é chegado. Louvae ao Senhor.

< Zabura 148 >