< Zabura 147 >

1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Looft den HEERE, want onzen God te psalmzingen is goed, dewijl Hij liefelijk is; de lof is betamelijk.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
De HEERE bouwt Jeruzalem; Hij vergadert Israels verdrevenen.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
Hij geneest de gebrokenen van hart, en Hij verbindt hen in hun smarten.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
Hij telt het getal der sterren; Hij noemt ze allen bij namen.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Onze Heere is groot en van veel kracht; Zijns verstands is geen getal.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
De HEERE houdt de zachtmoedigen staande; de goddelozen vernedert Hij, tot de aarde toe.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Zingt den HEERE bij beurte met dankzegging; psalmzingt onzen God op de harp.
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
Die de hemelen met wolken bedekt, Die voor de aarde regen bereidt; Die het gras op de bergen doet uitspruiten;
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
Die het vee zijn voeder geeft; aan de jonge raven, als zij roepen.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
Hij heeft geen lust aan de sterkte des paards; Hij heeft geen welgevallen aan de benen des mans.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
De HEERE heeft een welgevallen aan hen, die Hem vrezen, die op Zijn goedertierenheid hopen.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
O Jeruzalem! roem den HEERE; o Sion! loof uw God.
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
Want Hij maakt de grendelen uwer poorten sterk; Hij zegent uw kinderen binnen in u.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
Die uw landpalen in vrede stelt; Hij verzadigt u met het vette der tarwe.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
Hij zendt Zijn bevel op aarde; Zijn woord loopt zeer snel.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
Hij geeft sneeuw als wol; Hij strooit den rijm als as.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
Hij werpt Zijn ijs heen als stukken; wie zou bestaan voor Zijn koude?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
Hij zendt Zijn woord, en doet ze smelten; Hij doet Zijn wind waaien, de wateren vloeien henen.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
Hij maakt Jakob Zijn woorden bekend, Israel Zijn inzettingen en Zijn rechten.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
Alzo heeft Hij geen volk gedaan; en Zijn rechten, die kennen zij niet. Hallelujah!

< Zabura 147 >