< Zabura 146 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Praise ye Jehovah. Praise Jehovah, O my soul.
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
While I live will I praise Jehovah: I will sing praises unto my God while I have any being.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Put not your trust in princes, Nor in the son of man, in whom there is no help.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
His breath goeth forth, he returneth to his earth; In that very day his thoughts perish.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Happy is he that hath the God of Jacob for his help, Whose hope is in Jehovah his God:
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
Who made heaven and earth, The sea, and all that in them is; Who keepeth truth for ever;
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
Who executeth justice for the oppressed; Who giveth food to the hungry. Jehovah looseth the prisoners;
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
Jehovah openeth [the eyes of] the blind; Jehovah raiseth up them that are bowed down; Jehovah loveth the righteous;
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
Jehovah preserveth the sojourners; He upholdeth the fatherless and widow; But the way of the wicked he turneth upside down.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
Jehovah will reign for ever, Thy God, O Zion, unto all generations. Praise ye Jehovah.