< Zabura 145 >

1 Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
Déjame glorificarte, oh Dios, mi Rey; y bendecir tu nombre por los siglos de los siglos.
2 Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
Todos los días te daré bendición, alabando tu nombre por los siglos de los siglos.
3 Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
Grande es el Señor, y muy digno de alabanza; su poder excede nuestro entendimiento.
4 Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
Una generación tras otra alabarán tus grandes actos y dejarán en claro el funcionamiento de tu fortaleza.
5 Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
Mis pensamientos serán del honor y la gloria de tu gobierno y de la maravilla de tus obras.
6 Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
Los hombres hablarán del poder y temor de tus actos; Daré noticias de tu gloria.
7 Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
Sus dichos estarán llenos del recuerdo de toda tu misericordia, y ellos harán canciones de tu justicia.
8 Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
El Señor está lleno de gracia y compasión; lento para enojarse, pero grande en misericordia.
9 Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
El Señor es bueno con todos los hombres; y sus misericordias son sobre todas sus obras.
10 Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
Todas las obras de tus manos te alaban, oh Señor; y tus santos te dan bendición.
11 Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
Sus palabras serán de la gloria de tu reino y de sus palabras sobre tu fortaleza;
12 saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
Para que los hijos de los hombres conozcan sus actos de poder y la gran gloria de su reino.
13 Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
Tu reino es un reino eterno, y tu gobierno es por todas las generaciones.
14 Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
El Señor es el sostén de todos los que caen y el levanta a todos los oprimidos.
15 Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
Los ojos de todos los hombres te esperan; y les das su comida a su tiempo.
16 Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
Con la apertura de tu mano, todo ser vivo tiene su deseo en toda su plenitud.
17 Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
El Señor es recto en todos sus caminos, y amable en todas sus obras.
18 Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
El Señor está cerca de todos los que le dan honor a su nombre; de todos los que le dan honor con verdaderos corazones.
19 Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
A sus adoradores, les dará su deseo; su clamor llega a sus oídos, y él les da salvación.
20 Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
El Señor guardará a todos sus adoradores del peligro; pero él enviará destrucción a todos los pecadores.
21 Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.
Mi boca alabará al Señor; que todos bendigan su santo nombre por los siglos de los siglos.

< Zabura 145 >