< Zabura 140 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
Müzik şefi için - Davut'un mezmuru Ya RAB, kurtar beni kötü insandan, Koru beni zorbadan.
2 masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
Onlar yüreklerinde kötülük tasarlar, Savaşı sürekli körükler,
3 Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
Yılan gibi dillerini bilerler, Engerek zehiri var dudaklarının altında. (Sela)
4 Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
Ya RAB, sakın beni kötünün elinden, Koru beni zorbadan; Bana çelme takmayı tasarlıyorlar.
5 Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
Küstahlar benim için tuzak kurdu, Haydutlar ağ gerdi; Yol kenarına kapan koydular benim için. (Sela)
6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
Sana diyorum, ya RAB: “Tanrım sensin.” Yalvarışıma kulak ver, ya RAB.
7 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
Ey Egemen RAB, güçlü kurtarıcım, Savaş gününde başımı korudun.
8 Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
Kötülerin dileklerini yerine getirme, ya RAB, Tasarılarını ileri götürme! Yoksa gurura kapılırlar. (Sela)
9 Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
Beni kuşatanların başını, Dudaklarından dökülen fesat kaplasın.
10 Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
Kızgın korlar yağsın üzerlerine! Ateşe, dipsiz çukurlara atılsınlar, Bir daha kalkamasınlar.
11 Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
İftiracılara ülkede hayat kalmasın, Felaket zorbaları amansızca avlasın.
12 Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
Biliyorum, RAB mazlumun davasını savunur, Yoksulları haklı çıkarır.
13 Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.
Kuşkusuz doğrular senin adına şükredecek, Dürüstler senin huzurunda oturacak.

< Zabura 140 >