< Zabura 140 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
Au chef des chantres. Psaume de David. Délivre-moi, Eternel, des gens méchants, protège-moi contre les hommes de violence,
2 masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
qui conçoivent de mauvais desseins dans leur cœur, chaque jour fomentent des guerres.
3 Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
Ils affilent leur langue comme un serpent, un venin de vipère se glisse sous leurs lèvres. (Sélah)
4 Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
Garde-moi, Seigneur, des mains du méchant! Protège-moi contre les hommes de violence, qui se proposent de me faire trébucher dans ma marche.
5 Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
Des présomptueux dressent pièges et lacets contre moi; tendent des filets le long de la route, me posent des embûches. (Sélah)
6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
Mais j’ai dit à l’Eternel: "Tu es mon Dieu: prête l’oreille, Seigneur, à mes cris suppliants!"
7 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
O Dieu, mon Maître, mon aide puissante, tu couvres ma tête de ta protection au jour du combat.
8 Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
N’Accorde pas, Eternel, les demandes des méchants, ne laisse point s’accomplir leurs perfides desseins; ils lèveraient trop haut, (Sélah)
9 Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
leur tête, ceux qui m’enserrent; que la méchanceté de leurs lèvres les enveloppe tout entiers!
10 Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
Que des charbons ardents pleuvent sur eux, qu’on les précipite dans les flammes, dans des gouffres d’où ils ne puissent s’échapper!
11 Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
Que l’homme à la langue perfide n’ait point d’avenir dans le pays l Que l’homme de violence soit entraîné par sa méchanceté dans la chute!
12 Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
Je le sais, l’Eternel défend la cause du pauvre, le droit des humbles.
13 Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.
Oui certes, les justes auront à rendre hommage à ton nom, les gens de bien séjourneront devant ta face!

< Zabura 140 >