< Zabura 139 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
Müzik şefi için - Davut'un mezmuru Ya RAB, sınayıp tanıdın beni.
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
Oturup kalkışımı bilirsin, Niyetimi uzaktan anlarsın.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
Gittiğim yolu, yattığım yeri inceden inceye elersin, Bütün yaptıklarımdan haberin var.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
Daha sözü ağzıma almadan, Söyleyeceğim her şeyi bilirsin, ya RAB.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
Beni çepeçevre kuşattın, Elini üzerime koydun.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Kaldıramam böylesi bir bilgiyi, Başa çıkamam, erişemem.
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Nereye gidebilirim senin Ruhun'dan, Nereye kaçabilirim huzurundan?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
Göklere çıksam, oradasın, Ölüler diyarına yatak sersem, yine oradasın. (Sheol h7585)
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
Seherin kanatlarını alıp uçsam, Denizin ötesine konsam,
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
Orada bile elin yol gösterir bana, Sağ elin tutar beni.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
Desem ki, “Karanlık beni kaplasın, Çevremdeki aydınlık geceye dönsün.”
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
Karanlık bile karanlık sayılmaz senin için, Gece, gündüz gibi ışıldar, Karanlıkla aydınlık birdir senin için.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
İç varlığımı sen yarattın, Annemin rahminde beni sen ördün.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
Sana övgüler sunarım, Çünkü müthiş ve harika yaratılmışım. Ne harika işlerin var! Bunu çok iyi bilirim.
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
Gizli yerde yaratıldığımda, Yerin derinliklerinde örüldüğümde, Bedenim senden gizli değildi.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Henüz döl yatağındayken gözlerin gördü beni; Bana ayrılan günlerin hiçbiri gelmeden, Hepsi senin kitabına yazılmıştı.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
Hakkımdaki düşüncelerin ne değerli, ey Tanrı, Sayıları ne çok!
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
Kum tanelerinden fazladır saymaya kalksam. Uyanıyorum, hâlâ seninleyim.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
Ey Tanrı, keşke kötüleri öldürsen! Ey eli kanlı insanlar, uzaklaşın benden!
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
Çünkü senin için kötü konuşuyorlar, Adını kötüye kullanıyor düşmanların.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Ya RAB, nasıl tiksinmem senden tiksinenlerden? Nasıl iğrenmem sana başkaldıranlardan?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
Onlardan tümüyle nefret ediyor, Onları düşman sayıyorum.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Ey Tanrı, yokla beni, tanı yüreğimi, Sına beni, öğren kaygılarımı.
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
Bak, seni gücendiren bir yönüm var mı, Öncülük et bana sonsuz yaşam yolunda!

< Zabura 139 >