< Zabura 139 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
O lord, you have searched me, and known me.
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
You know my sitting down and mine rising up, you understand my thought far off.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
You compass my path and my lying down, and are acquainted with all my ways.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
For there is not a word in my tongue, but, lo, O LORD, you know it altogether.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
You have beset me behind and before, and laid your hand upon me.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Such knowledge is too wonderful for me; it is high, I cannot attain unto it.
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Where shall I go from your spirit? or where shall I flee from your presence?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
If I ascend up into heaven, you are there: if I make my bed in hell, behold, you are there. (Sheol h7585)
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
If I take the wings of the morning, and dwell in the uttermost parts of the sea;
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
Even there shall your hand lead me, and your right hand shall hold me.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
If I say, Surely the darkness shall cover me; even the night shall be light about me.
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
Yea, the darkness hides not from you; but the night shines as the day: the darkness and the light are both alike to you.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
For you have possessed my reins: you have covered me in my mother's womb.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
I will praise you; for I am fearfully and wonderfully made: marvellous are your works; and that my soul knows right well.
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
My substance was not hid from you, when I was made in secret, and curiously wrought in the low parts of the earth.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
your eyes did see my substance, yet being imperfect; and in your book all my members were written, which in continuance were fashioned, when as yet there was none of them.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
How precious also are your thoughts unto me, O God! how great is the sum of them!
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
If I should count them, they are more in number than the sand: when I awake, I am still with you.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
Surely you will slay the wicked, O God: depart from me therefore, all of you bloody men.
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
For they speak against you wickedly, and your enemies take your name in vain.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Do not I hate them, O LORD, that hate you? and am not I grieved with those that rise up against you?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
I hate them with perfect hatred: I count them mine enemies.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Search me, O God, and know my heart: try me, and know my thoughts:
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
And see if there be any wicked way in me, and lead me in the way everlasting.

< Zabura 139 >