< Zabura 137 >

1 A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
By rivers of Babylon—There we sat, Indeed, we wept when we remembered Zion.
2 A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
We hung our harps on willows in its midst.
3 gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
For there our captors asked us the words of a song, And our spoilers—joy: “Sing to us of a song of Zion.”
4 Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
How do we sing the song of YHWH, On the land of a stranger?
5 In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
If I forget you, O Jerusalem, my right hand forgets!
6 Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
My tongue cleaves to my palate, If I do not remember you, If I do not exalt Jerusalem above my chief joy.
7 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
Remember, YHWH, for the sons of Edom, The day of Jerusalem, Those saying, “Raze, raze to its foundation!”
8 Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
O daughter of Babylon, O destroyed one, O the blessedness of him who repays to you your deed, That you have done to us.
9 shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.
O the blessedness of him who seizes, and has dashed your sucklings on the rock!

< Zabura 137 >