< Zabura 135 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
alleluia laudate nomen Domini laudate servi Dominum
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
qui statis in domo Domini in atriis domus Dei nostri
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
laudate Dominum quia bonus Dominus psallite nomini eius quoniam suave
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
quoniam Iacob elegit sibi Dominus Israhel in possessionem sibi
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
quia ego cognovi quod magnus est Dominus et Deus noster prae omnibus diis
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
omnia quae voluit Dominus fecit in caelo et in terra in mare et in omnibus abyssis
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
educens nubes ab extremo terrae fulgora in pluviam fecit qui producit ventos de thesauris suis
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
qui percussit primogenita Aegypti ab homine usque ad pecus
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
emisit signa et prodigia in medio tui Aegypte in Pharaonem et in omnes servos eius
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
qui percussit gentes multas et occidit reges fortes
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
Seon regem Amorreorum et Og regem Basan et omnia regna Chanaan
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
et dedit terram eorum hereditatem hereditatem Israhel populo suo
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
Domine nomen tuum in aeternum Domine memoriale tuum in generationem et generationem
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
quia iudicabit Dominus populum suum et in servis suis deprecabitur
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
simulacra gentium argentum et aurum opera manuum hominum
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
os habent et non loquentur oculos habent et non videbunt
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
aures habent et non audient neque enim est spiritus in ore eorum
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
similes illis fiant qui faciunt ea et omnes qui sperant in eis
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
domus Israhel benedicite Domino domus Aaron benedicite Domino
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
domus Levi benedicite Domino qui timetis Dominum benedicite Domino
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
benedictus Dominus ex Sion qui habitat in Hierusalem