< Zabura 135 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Louez l’Éternel! Louez le nom de l’Éternel, Louez-le, serviteurs de l’Éternel,
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
Qui vous tenez dans la maison de l’Éternel, Dans les parvis de la maison de notre Dieu!
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Louez l’Éternel! Car l’Éternel est bon. Chantez à son nom! Car il est favorable.
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
Car l’Éternel s’est choisi Jacob, Israël, pour qu’il lui appartînt.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
Je sais que l’Éternel est grand, Et que notre Seigneur est au-dessus de tous les dieux.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
Tout ce que l’Éternel veut, il le fait, Dans les cieux et sur la terre, Dans les mers et dans tous les abîmes.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
Il fait monter les nuages des extrémités de la terre, Il produit les éclairs et la pluie, Il tire le vent de ses trésors.
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
Il frappa les premiers-nés de l’Égypte, Depuis les hommes jusqu’aux animaux.
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
Il envoya des signes et des miracles au milieu de toi, Égypte! Contre Pharaon et contre tous ses serviteurs.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
Il frappa des nations nombreuses, Et tua des rois puissants,
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
Sihon, roi des Amoréens, Og, roi de Basan, Et tous les rois de Canaan;
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
Et il donna leur pays en héritage, En héritage à Israël, son peuple.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
Éternel! Ton nom subsiste à toujours, Éternel! ta mémoire dure de génération en génération.
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
Car l’Éternel jugera son peuple, Et il aura pitié de ses serviteurs.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
Les idoles des nations sont de l’argent et de l’or, Elles sont l’ouvrage de la main des hommes.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Elles ont une bouche et ne parlent point, Elles ont des yeux et ne voient point,
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
Elles ont des oreilles et n’entendent point, Elles n’ont point de souffle dans leur bouche.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Ils leur ressemblent, ceux qui les fabriquent, Tous ceux qui se confient en elles.
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
Maison d’Israël, bénissez l’Éternel! Maison d’Aaron, bénissez l’Éternel!
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
Maison de Lévi, bénissez l’Éternel! Vous qui craignez l’Éternel, bénissez l’Éternel!
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Que de Sion l’on bénisse l’Éternel, Qui habite à Jérusalem! Louez l’Éternel!

< Zabura 135 >