< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Ein Stufenlied. Aus den Tiefen rufe ich zu dir, Jehova!
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Herr, höre auf meine Stimme! Laß deine Ohren aufmerksam sein auf die Stimme meines Flehens!
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Wenn du, Jehova, merkst auf die Ungerechtigkeiten: Herr, wer wird bestehen?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Doch bei dir ist Vergebung, damit du gefürchtet werdest.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
Ich warte auf Jehova, meine Seele wartet; und auf sein Wort harre ich.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
Meine Seele harrt auf den Herrn, mehr als die Wächter auf den Morgen, die Wächter auf den Morgen.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Harre, Israel, auf Jehova! Denn bei Jehova ist die Güte, und viel Erlösung bei ihm.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
Und er, er wird Israel erlösen von allen seinen Ungerechtigkeiten.

< Zabura 130 >