< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Cantique des montées. Du fond de l'abîme je crie vers toi, Yahweh.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Seigneur, écoute ma voix; que tes oreilles soient attentives aux accents de ma prière!
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Si tu gardes le souvenir de l'iniquité, Yahweh, Seigneur, qui pourra subsister?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Mais auprès de toi est le pardon, afin qu'on te révère.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
J'espère en Yahweh; mon âme espère, et j'attends sa parole.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
Mon âme aspire après le Seigneur plus que les guetteurs n'aspirent après l'aurore.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Israël, mets ton espoir en Yahweh! Car avec Yahweh est la miséricorde, avec lui une surabondante délivrance.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
C'est lui qui rachètera Israël de toutes ses iniquités.

< Zabura 130 >