< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
A Song of Ascents. Out of the depths have I called Thee, O LORD.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Lord, hearken unto my voice; let Thine ears be attentive to the voice of my supplications.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
If Thou, LORD, shouldest mark iniquities, O Lord, who could stand?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
For with Thee there is forgiveness, that Thou mayest be feared.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
I wait for the LORD, my soul doth wait, and in His word do I hope.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
My soul waiteth for the Lord, more than watchmen for the morning; yea, more than watchmen for the morning.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
O Israel, hope in the LORD; for with the LORD there is mercy, and with Him is plenteous redemption.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
And He will redeem Israel from all his iniquities.

< Zabura 130 >