< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
上行之诗。 耶和华啊,我从深处向你求告!
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
主啊,求你听我的声音! 愿你侧耳听我恳求的声音!
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
主—耶和华啊,你若究察罪孽, 谁能站得住呢?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
但在你有赦免之恩, 要叫人敬畏你。
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
我等候耶和华,我的心等候; 我也仰望他的话。
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
我的心等候主, 胜于守夜的,等候天亮, 胜于守夜的,等候天亮。
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
以色列啊,你当仰望耶和华! 因他有慈爱,有丰盛的救恩。
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
他必救赎以色列脱离一切的罪孽。

< Zabura 130 >