< Zabura 126 >

1 Waƙar haurawa. Sa’ad da Ubangiji ya dawo da kamammu zuwa Sihiyona, mun kasance kamar mutanen da suka yi mafarki.
Cuando el Señor hizo un cambio en el destino de Sión, éramos como hombres en un sueño.
2 Bakunanmu sun cika da dariya, harsunanmu da waƙoƙin farin ciki. Sai ana faɗi a cikin al’ummai, “Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominsu.”
Entonces nuestras bocas se llenaron de risa, y nuestras lenguas dieron un alegre clamor; dijeron entre las naciones: Jehová hizo grandes cosas por ellos.
3 Ubangiji ya aikata manyan abubuwa dominmu, mun kuwa cika da farin ciki.
El Señor hizo grandes cosas por nosotros; por lo cual estamos contentos.
4 Ka maido da wadatarmu, ya Ubangiji kamar rafuffuka a Negeb.
Deja que nuestro destino sea cambiado, Señor, como las corrientes en el sur.
5 Waɗanda suka yi shuka da hawaye za su yi girbi da waƙoƙin farin ciki.
Los que sembraron con llanto, cosecharan en el grano con gritos de alegría.
6 Shi da ya fita yana kuka, riƙe da iri don shuki, zai dawo da waƙoƙin farin ciki, ɗauke da dammuna.
Aunque un hombre salga llorando, llevando consigo su bolsa de semilla; él vendrá de nuevo en alegría, con los tallos de grano en sus brazos.

< Zabura 126 >