< Zabura 122 >

1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
Alegrei-me quando me disseram: Vamos á casa do Senhor.
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Os nossos pés estão dentro das tuas portas, ó Jerusalem.
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jerusalem está edificada como uma cidade que é compacta,
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
Onde sobem as tribus, as tribus do Senhor, até o testemunho d'Israel, para darem graças ao nome do Senhor.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
Pois ali estão os thronos do juizo, os thronos da casa de David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Orae pela paz de Jerusalem: prosperarão aquelles que te amam.
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Haja paz dentro de teus muros, e prosperidade dentro dos teus palacios.
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
Por causa dos meus irmãos e amigos, direi: Paz esteja em ti.
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
Por causa da casa do Senhor, nosso Deus, buscarei o teu bem.

< Zabura 122 >