< Zabura 122 >
1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
Cantique de Maaloth, de David. Je me réjouis lorsqu'on me dit: Allons à la maison de l'Éternel!
2 Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
Nos pieds s'arrêtent dans tes portes, ô Jérusalem!
3 An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
Jérusalem, qui es bâtie comme une ville aux édifices pressés.
4 A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
C'est là que montent les tribus, les tribus de l'Éternel, ce qui est un témoignage en Israël, pour célébrer le nom de l'Éternel.
5 A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
C'est là que sont dressés les trônes pour la justice, les trônes pour la maison de David.
6 Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
Priez pour la paix de Jérusalem! Que ceux qui t'aiment jouissent de la paix!
7 Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
Que la paix soit dans tes murs, et le repos dans tes palais!
8 Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
A cause de mes frères et de mes amis, je prierai pour ta paix.
9 Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.
A cause de la maison de l'Éternel notre Dieu, je demanderai pour toi le bonheur.