< Zabura 121 >

1 Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
I will lift up my eyes to the mountains. From where shall my help come?
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
My help is from Jehovah, who made heaven and earth.
3 Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
He will not allow thy foot to be moved. He who keeps thee will not slumber.
4 tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
Behold, he who keeps Israel will neither slumber nor sleep.
5 Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
Jehovah is thy keeper. Jehovah is thy shade upon thy right hand.
6 rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
The sun shall not smite thee by day, nor the moon by night.
7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
Jehovah will keep thee from all evil. He will keep thy soul.
8 Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.
Jehovah will keep thy going out and thy coming in from this time forth and for evermore.

< Zabura 121 >