< Zabura 120 >

1 Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
Ein Stufenlied. - In meiner Drangsal rufe ich zum Herrn. Er hört auf mich.
2 Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
Herr! Rette mich von Lügenlippen, von trügerischer Zunge!
3 Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
Wie liefert Dir die trügerische Zunge fort und fort
4 Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
geschärfte Pfeile eines Helden samt Ginsterkohlen!
5 Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
Weh mir, daß ich bei Mesech gaste, bei Kedars Zelten weile!
6 Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
Zu lange schon weilt meine Seele bei Friedensfeinden.
7 Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.
Ich bin so friedsam. Doch, wenn ich's auch noch so sehr beteure, sie wollen Kampf.

< Zabura 120 >