< Zabura 119 >

1 Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
Glückselig, die unsträflich leben und in des Herrn Gesetzen wandeln!
2 Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
Glückselig sind, die seine Bräuche achten und ihn von ganzem Herzen suchen,
3 Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
die nie ein Unrecht tun und die auf seinen Wegen wandeln!
4 Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Du selbst gibst Deine Vorschriften, daß man genau sie halte.
5 Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
Ach, wäre fest mein Wandel in der Befolgung Deiner Ordnungen!
6 Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Dann werde ich niemals zuschanden, beacht ich alle Deine Satzungen.
7 Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
Ich danke Dir von Herzensgrunde, wenn ich erlerne Deine so gerechten Weisungen.
8 Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
Genau beachten will ich Deine Vorschriften. Verlaß mich nicht dabei!
9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
Wodurch erhält ein Jüngling seinen Wandel rein? Wenn er sich hält an Deine Worte.
10 Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
Von ganzem Herzen suche ich Dich auf. Entfremde mich nicht Deinen Satzungen!
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
In meinem Herzen berge ich Dein Wort, auf daß ich wider Dich nicht sündige.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Gepriesen seist Du, Herr! Gewöhne mich an Deine Ordnungen!
13 Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
Auswendig sag ich auf all Deine mündlichen Gebote.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
Ich freue mich des Weges hin zu Deinen Zeugnissen weit mehr als über irgendwelche Schätze.
15 Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
Was Du befiehlst, dem sinn ich nach und schaue hin auf Deine Pfade.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
Mit Deinen Ordnungen befasse ich mich gern, vergesse nicht Dein Wort.
17 Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
Gewähre Deinem Knechte, daß ich leben bleibe! Dann halte ich Dein Wort.
18 Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Entschleiere mir das Auge, daß ich schaue, was wunderbar an Deiner Lehre!
19 Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
Ein Fremdling bin ich in dem Lande. Verbirg mir nimmer Deine Satzungen!
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
In Sehnsucht meine Seele sich verzehrt nach Deinen Weisungen zu jeder Zeit.
21 Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Du schiltst die Frechen. Verfluchst, die Deine Satzungen mißachten!
22 Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Wend Spott und Hohn von mir; denn Deine Zeugnisse, ich achte sie!
23 Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
Ob Fürsten auch sich wider mich beraten, Dein Knecht beherzigt dennoch Deine Ordnungen.
24 Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
Ja, Wonne sind mir Deine Zeugnisse, Wegweiser sind mir Deine Vorschriften.
25 An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Am Staube klebe ich. Erhalte mich nach Deinem Wort am Leben!
26 Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
Ich lege meine Wege dar, und Du erhörst mich. Gewöhne mich an Deine Satzungen!
27 Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
Gib Einsicht mir ins Wesen Deiner Vorschriften! Dann will ich Deine Wunder überdenken.
28 Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
Vor Leid weint meine Seele. Richt mich nach Deinem Worte auf!
29 Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
Halt fern von mir den Pfad der Untreue! Zu eigen gib mir Deine Lehre gnädiglich!
30 Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
Den Weg der Treue wähle ich, befolge Deine Weisungen.
31 Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
Ich hänge fest an Deinen Zeugnissen. Herr, laß mich nicht zuschanden werden!
32 Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
Ich laufe auf dem Wege Deiner Ordnungen; Du machst mir weit das Herz.
33 Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
Zeig mir den Weg zu Deinen Vorschriften, o Herr! Ich will ihn mit Bedacht einhalten.
34 Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
Gib Einsicht mir, daß ich befolge Deine Lehre und sie mit ganzem Herzen hüte!
35 Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
Laß Deiner Satzung Pfad mich wallen! Denn Freude habe ich daran.
36 Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
Zu Deinen Bräuchen lenke hin mein Herz und nicht zur Eigenliebe!
37 Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Lenk meine Augen ab vom Schielen nach dem Eitlen! Auf Deinen Wegen laß mich Leben finden!
38 Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
Bewähr an Deinem Knecht Dein Wort, das zu der Ehrfurcht vor Dir leiten soll!
39 Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
Nimm meine Schmach hinweg, daß ich gezweifelt, ob Deine Weisungen auch heilsam seien!
40 Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
Nach Deinen Vorschriften verlangt es mich. In Deiner Liebe laß mich leben!
41 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
Herr! Deine Gnade komme über mich, Dein Heil nach Deinem Worte,
42 sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
daß ich entgegne meinem Schmäher! Denn Deinem Wort vertraue ich.
43 Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
Versag nicht meinem Mund das rechte Wort! Auf Deine Weisung harr ich sehnsuchtsvoll.
44 Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
Stets will ich Deiner Lehre folgen, für immer und auf ewig,
45 Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
nach ihr, der überreichen, wandeln. Nach Deinen Vorschriften verlangt es mich.
46 Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
Vor Königen selbst rede ich von Deinen Zeugnissen ohn alle Scheu.
47 gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
Ich habe meine Lust an Deinen Satzungen; ich liebe sie.
48 Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
Ich rege meine Hände eifervoll für Deine so geliebten Satzungen und sinne über Deine Ordnungen.
49 Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
Gedenke Deinem Diener jenes Wort, auf das Du mich fest hoffen lässest!
50 Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
Dies ist mein Trost in meinem Leid, daß Lebensmut Dein Wort mir gibt.
51 Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
So sehr Vermessene meiner spotten, ich weiche nicht von Deiner Lehre.
52 Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
An Deine Weisungen, die alten, denke ich und fühle mich getröstet, Herr.
53 Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
Der Frevler wegen packt mich Zornesglut, die Deine Lehre schnöd verlassen.
54 Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
Zu Lobesliedern sind mir Deine Ordnungen geworden im Haus, wo ich als Fremdling weile.
55 Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
Ich denke, Herr, an Deinen Namen in der Nacht, an Deine Lehre selbst in mitternächtiger Stunde.
56 Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
Zum Grundsatz ward mir dies, weil ich um Deine Vorschriften mich kümmere:
57 Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
"Mein Alles ist der Herr", das deut ich so: Ich muß die Worte Dein beachten.
58 Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
Von ganzem Herzen werbe ich um Deine Huld. Sei gnädig mir nach Deinem Wort!
59 Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
Ich überlege meine Wege und lenke meine Füß hin zu Deinen Zeugnissen.
60 Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
Ich eile, säume nicht, zu halten Deine Satzungen.
61 Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
Der Frevler Stricke wollen mich umfangen; doch ich vergesse nimmer Deine Lehre.
62 Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
Um Mitternacht erhebe ich mich schon und danke Dir für Deine Weisungen, die so gerecht,
63 Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
im Wetteifer mit allen, die Dich fürchten, die Deine Vorschriften befolgen.
64 Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Voll Deiner Gnade ist die Erde, Herr. Gewöhne mich an Deine Satzungen!
65 Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
Du tust an Deinem Knechte Gutes, nach Deinem Worte, Herr.
66 Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
So lehre mich heilsame Sitte und Erkenntnis! Denn Deinen Satzungen vertraue ich.
67 Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
Bevor ich leiden mußte, irrte ich; nun aber halte ich Dein Wort.
68 Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
Du bist so gut und handelst gut. Gewöhne mich an Deine Satzungen!
69 Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
Mir dichten Freche Falsches an; ich aber halte Deine Vorschriften aus ganzem Herzen.
70 Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
Ihr Herz ist stumpf wie Fett; doch ich ergötze mich an Deiner Lehre.
71 Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
Mir war es heilsam, daß ich litt, damit ich mich an Deine Ordnungen gewöhnte.
72 Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
Dein mündliches Gesetz gilt mir weit mehr als tausend Stücke Gold und Silber.
73 Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
Von Deiner Hand bin ich geschaffen und gebildet. Verleih mir Einsicht, daß ich mich an Deine Satzungen gewöhne!
74 Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
Mit Freuden sehen, die Dich fürchten, daß ich mich auf Dein Wort verlasse.
75 Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
Ich weiß es, Herr: Gerecht sind Deine Weisungen; in bester Absicht hast Du mich gezüchtigt.
76 Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
Zum Troste sei mir Deine Huld, wie Deinem Knechte Du verheißen
77 Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
Laß Dein Erbarmen mich erquicken! Denn Deine Lehre ist mir Lust.
78 Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
Schmach über diese Frechen, weil grundlos sie zu Unrecht mich bezichtigen! Ich sinne über Deine Vorschriften.
79 Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
Sie mögen sich durch mich in solche wandeln, die fürchten Dich und schätzen lernen Deine Zeugnisse!
80 Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
Unfehlbar sei mein Herz in Deinen Ordnungen, damit ich nicht erröten muß!
81 Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
Nach Deinem Heile schmachtet meine Seele, ich harre Deines Wortes.
82 Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
Nach Deinem Worte schmachten meine Augen: "Wann bringt's mir Trost?"
83 Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
Bin ich auch wie ein Schlauch im Rauche, vergesse ich doch niemals Deine Ordnungen.
84 Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
Wieviel sind noch der Tage Deines Knechtes? Wann richtest Du, die mich verfolgen?
85 Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
Mir graben Freche Gruben in dem, was Deiner Lehre nicht entspricht.
86 Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
Was Du befiehlst, ist lautre Wahrheit; grundlos verfolgt man mich. Komm mir zu Hilfe!
87 Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
Beinah vertilgten sie mich von der Erde; doch laß ich nicht von Deinen Vorschriften.
88 Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
Nach Deiner Huld erhalte mich am Leben, daß Deines Mundes Lehre ich befolge!
89 Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
Dein Wort ist für die Ewigkeiten, Herr; dem Himmel gleich, so steht es fest gegründet.
90 Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
Durch alle Zeiten währet Deine Treue, wie Du die Erde für die Dauer hast gegründet.
91 Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
Für Deine Winke steht sie heut bereit; denn alles ist Dir untertan.
92 Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
Wenn Deine Lehre mir nicht Wonne wäre, vergangen wäre ich in meinem Leid.
93 Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
Nie will ich Deine Vorschriften vergessen; denn Du verleihst mir dadurch Lebenskraft.
94 Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
Dein bin ich. Steh mir bei! Denn ich durchforsche Deine Vorschriften.
95 Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
Mir lauern Frevler auf, mich umzubringen; doch ich vertiefe mich in Deine Zeugnisse.
96 Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
Bei allem anderen, was enden soll, ersehe ich ein Ende; doch Dein Gebot ist übergroß.
97 Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
Wie lieb ich Deine Lehre! Sie ist mein täglich Sinnen.
98 Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
Mich macht weit klüger Deine Satzung, als meine Feinde sind; denn ich besitze sie für immer.
99 Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
Verständiger noch werde ich als alle meine Lehrer; denn Deine Zeugnisse sind all mein Sinnen.
100 Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
An Einsicht übertreff ich Greise; denn ich beachte Deine Satzungen.
101 Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
Ich wehre meinem Fuße jeden bösen Weg, auf daß ich Deines Wortes pflege.
102 Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
Ich weiche nicht von deinen Weisungen; denn Du belehrest mich.
103 Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
Wie süß sind meinem Gaumen Deine Worte, weit süßer meinem Mund als Honigseim!
104 Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
Verständig werde ich durch Deine Vorschriften; drum hasse ich auch jeden falschen Pfad.
105 Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
Dein Wort ist meines Fußes Leuchte, ein Licht auf meinem Pfade.
106 Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
Ich hab's mir eidlich vorgenommen, was Du gerecht befohlen, auch zu halten.
107 Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
Ich bin gar tief gebeugt. Nach Deinem Worte, Herr, belebe mich!
108 Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
Laß, Herr, Dir meines Mundes Übungen gefallen! Gewöhne mich an Deine Weisungen!
109 Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
Mein Leben ist beständig in Gefahr; doch ich vergesse Deine Lehre nicht.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
Mir legen Frevler Schlingen; ich irre nimmer ab von Deinen Vorschriften. -
111 Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
Ein ewig Erbgut sind mir Deine Zeugnisse; ja, Herzenswonne sind sie mir.
112 Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
Ich neige hin mein Herz, zu tun, was Du befiehlst, für immer auf das eifrigste.
113 Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
Ich hasse Zweifler; doch Deine Lehre liebe ich.
114 Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
Mein Schirm und Schild bist Du; ich harre Deines Wortes.
115 Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Hinweg von mir, ihr Übeltäter! Ich will ja meines Gottes Satzungen befolgen.
116 Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Nach Deinem Worte stärke mich, auf daß ich lebe! Beschäme mich in meiner Hoffnung nicht!
117 Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Halt Du mich fest, daß ich gerettet werde! Ich schaue stets nach Deinen Ordnungen.
118 Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Die sich vergehn an Deinen Ordnungen, die wirfst Du weg; denn Trug ist all ihr Sinnen.
119 Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
Die Frevler all auf Erden achtest Du wie Schlacken; drum liebe ich auch Deine Zeugnisse.
120 Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
Aus Furcht vor Dir erschaudert mir die Haut; Ich fürchte mich vor Deinen Strafgerichten.
121 Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
Das Rechte tu ich und das Gute. Gib meinen Drängern mich nicht preis!
122 Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Vertritt zu seinem Besten Deinen Knecht, daß nicht die Stolzen mir Gewalt antun!
123 Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Nach Deiner Hilfe schmachten meine Augen, nach Deiner Heilsverheißung.
124 Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Verfahr mit Deinem Knecht nach Deiner Huld! Gewöhne mich an Deine Ordnungen!
125 Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
Dein Knecht bin ich. Belehre mich, auf daß ich Deine Bräuche wohl verstehe!
126 Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
's ist Zeit, sich für den Herrn zu regen; sie wollen Dein Gesetz abschaffen.
127 Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
Drum liebe ich auch Deine Satzungen viel mehr als Gold, als selbst das feinste Gold.
128 saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
Drum habe ich all Deine Vorschriften mir auserwählt; ich hasse jeden falschen Weg.
129 Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
Geheimnisvoll sind Deine Zeugnisse drum achtet ihrer meine Seele.
130 Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
Dein Wort erschließen spendet Licht; es macht die Einfalt klug.
131 Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
Begierig öffne ich den Mund; denn mich verlangt nach Deinen Satzungen.
132 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Wend Dich zu mir und sei mir gnädig, wie's Rechtens ist für die, die Deinen Namen lieben!
133 Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
In Deinem Wort mach meine Schritte fest! Laß nicht das Böse herrschen über mich!
134 Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
Von Menschendruck befreie mich, damit ich Deine Vorschriften befolge!
135 Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Laß Deinem Knecht Dein Antlitz leuchten! Gewöhne mich an Deine Ordnungen!
136 Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Aus meinen Augen strömen Wasserbäche für die, die Deine Lehre nicht befolgen.
137 Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
Gerecht bist Du, o Herr, und Deine Weisungen sind recht.
138 Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Ganz recht sind Deine Bräuche, die Du bestimmst, und lauter Wahrheit.
139 Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
Mein Eifer zehrt mich auf, daß meine Gegner Deine Worte so vergessen.
140 An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Dein Wort ist rein geläutert; Dein Knecht hat's lieb.
141 Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
Gering, verachtet bin ich zwar; doch ich vergesse nimmer Deine Vorschriften.
142 Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Dein Recht bleibt ewig Recht; Wahrheit ist Deine Lehre.
143 Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
Mich treffen Not und Angst; doch Wonne sind mir Deine Satzungen.
144 Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Allzeit sind Deine Bräuche richtig. Gib Einsicht mir, daß ich am Leben bleibe!
145 Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
Von ganzem Herzen rufe ich: "Herr, höre mich! Ich möchte Deine Ordnungen befolgen!"
146 Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
"Hilf mir!" so rufe ich zu Dir. "Ich möchte Deine Zeugnisse beachten."
147 Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
Zur Zeit der Dämmerung erheb ich mich und flehe; ich harre Deines Wortes.
148 Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Bevor der Morgen graut, sind meine Augen wach, Dein Wort zu überdenken.
149 Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Nach Deiner Huld erhöre mein Gebet! Wie's Deine Art ist, laß mich leben!
150 Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
Die nach dem Laster jagen, kommen diesem immer näher und Deiner Lehre immer ferner.
151 Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Jedoch auch Du bist nahe, Herr; all Deine Satzungen sind Wahrheit.
152 Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
Von Urzeit her, so weiß ich es von Deinen Zeugnissen, Du hast sie eingesetzt für immer.
153 Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
Sieh her auf meine Not und rette mich! Ich habe Deine Lehre nicht vergessen.
154 Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Zu meiner Rettung führe meine Sache! Nach Deinem Worte laß mich leben!
155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
Den Frevlern ferne ist das Heil, weil sie nach Deinen Ordnungen nichts fragen.
156 Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Gar groß ist Dein Erbarmen, Herr. Laß mich, wie's Deine Art ist, leben!
157 Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Obschon mich viele drängen und verfolgen, so weiche ich doch nicht von Deinen Zeugnissen.
158 Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
Erblick ich Treulose, streit ich mit ihnen, dieweil Dein Wort sie nicht beachten.
159 Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
Wie gerne hab ich Deine Vorschriften! Erhalte mich nach Deiner Huld am Leben, Herr!
160 Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
Beständigkeit ist Deines Wortes Eigenart; für immer gelten Deine so gerechten Weisungen.
161 Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
Von Fürsten werd ich ohne Grund verfolgt; doch nur vor Deinem Worte bebt mein Herz.
162 Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
Ich freue mich ob Deines Wortes, wie der, so reiche Beute findet.
163 Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
Mit großem Abscheu hasse ich die Falschheit; nur Deine Lehre liebe ich.
164 Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
Ich preise Dich des Tages siebenmal für Deine so gerechten Weisungen.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
Die Deine Lehre lieben, ernten reichen Frieden; für sie gibt's keinen Anstoß mehr.
166 Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
Ich harre Deines Heiles, Herr, und Deine Satzungen befolge ich.
167 Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
Auf Deine Zeugnisse hat meine Seele acht und liebt sie über alle Maßen.
168 Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
Ich achte Deine Vorschriften und Bräuche; all meine Wege liegen ja vor Dir.
169 Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
Laß vor Dich kommen, Herr, mein Flehen! Nach Deinem Worte gib mir Einsicht!
170 Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
Mein Flehen komme vor Dein Angesicht! Errette mich nach Deinem Wort!
171 Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
Ein Loblied ström von meinen Lippen, gewöhnst Du mich an Deine Ordnungen!
172 Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
Dein Wort besinge meine Zunge! Denn alle Deine Satzungen sind Recht.
173 Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
Zum Beistand reiche mir die Hand! Denn Deine Vorschriften hab ich erwählt.
174 Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
Nach Deinem Heil verlangt's mich, Herr, und Wonne ist mir Deine Lehre.
175 Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
So möge leben meine Seele und Dich preisen, und dazu mögen mir verhelfen Deine Weisungen!
176 Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.
Wie ein verloren Schäflein irre ich umher. Such Deinen Knecht! Denn ich vergesse niemals Deine Satzungen.

< Zabura 119 >