< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
Amo al SEÑOR, porque ha oído mi voz y mis súplicas.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Porque ha inclinado a mí su oído, le invocaré en todos mis días.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Me rodearon los dolores de la muerte, me encontraron las angustias del sepulcro; angustia y dolor había yo hallado. (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Entonces invoqué el Nombre del SEÑOR, diciendo: Libra ahora, oh SEÑOR, mi alma.
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Clemente es el SEÑOR y justo; sí, misericordioso es nuestro Dios.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
El SEÑOR guarda a los simples; estaba debilitado, y me salvó.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Vuelve, oh alma mía, a tu reposo; porque el SEÑOR te ha hecho bien.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Porque has librado mi alma de la muerte, mis ojos de lágrimas, y mis pies de resbalar.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Andaré delante del SEÑOR en la tierra de los vivientes.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
Creí; por tanto hablé, y fui afligido en gran manera.
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Y dije en mi apresuramiento: Todo hombre es mentiroso.
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
¿Qué pagaré al SEÑOR por todos sus beneficios para conmigo?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
Tomaré la copa de la salud, e invocaré el Nombre del SEÑOR.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
Ahora pagaré mis votos al SEÑOR delante de todo su pueblo.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Estimada es en los ojos del SEÑOR la muerte de sus misericordiosos.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Así es oh SEÑOR, porque yo soy tu siervo, yo soy tu siervo, hijo de tu sierva; tú rompiste mis prisiones.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Te ofreceré sacrificio de alabanza, e invocaré el Nombre del SEÑOR.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
Ahora pagaré mis votos al SEÑOR delante de todo su pueblo;
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
en los atrios de la Casa del SEÑOR, en medio de ti, oh Jerusalén. Alelu-JAH.

< Zabura 116 >