< Zabura 115 >

1 Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
Not to us, O YHWH, not to us, But to Your Name give glory, For Your kindness, for Your truth.
2 Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
Why do the nations say, “Where, pray, [is] their God?”
3 Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
And our God [is] in the heavens, All that He has pleased He has done.
4 Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Their idols [are] silver and gold, work of man’s hands,
5 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
They have a mouth, and they do not speak, They have eyes, and they do not see,
6 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
They have ears, and they do not hear, They have a nose, and they do not smell,
7 suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
Their hands, but they do not handle, Their feet, and they do not walk;
8 Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
Nor do they mutter through their throat, Their makers are like them, Everyone who is trusting in them.
9 Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
O Israel, trust in YHWH, “He [is] their help and their shield.”
10 Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
O house of Aaron, trust in YHWH, “He [is] their help and their shield.”
11 Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
You fearing YHWH, trust in YHWH, “He [is] their help and their shield.”
12 Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
YHWH has remembered us, He blesses, He blesses the house of Israel, He blesses the house of Aaron,
13 zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
He blesses those fearing YHWH, The small with the great.
14 Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
YHWH adds to you—to you and to your sons.
15 Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
Blessed [are] you of YHWH, Maker of the heavens and earth,
16 Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
The heavens—the heavens [are] YHWH’s, And He has given the earth to sons of men;
17 Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
The dead do not praise YAH, Nor any going down to silence.
18 mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
And we, we bless YAH, From now on, and for all time. Praise YAH!

< Zabura 115 >