< Zabura 112 >

1 Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
Praise YAH! [ALEPH-BET] O the blessedness of one fearing YHWH, He has greatly delighted in His commands.
2 ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
His seed is mighty in the earth, The generation of the upright is blessed.
3 Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
Wealth and riches [are] in his house, And his righteousness is standing forever.
4 Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
Light has risen in darkness to the upright, Gracious, and merciful, and righteous.
5 Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
The man—good, gracious, and lending, He sustains his matters in judgment.
6 Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
For he is not moved for all time; For the righteous is a continuous memorial.
7 Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
He is not afraid of an evil report, His heart is prepared [and] confident in YHWH.
8 Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
His heart is sustained—he does not fear, Until he looks on his adversaries.
9 Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
He has scattered—has given to the needy, His righteousness is standing forever, His horn is exalted with glory.
10 Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.
The wicked sees, and has been angry, He gnashes his teeth, and has melted, The desire of the wicked perishes!

< Zabura 112 >