< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
Au chef des chantres. De David. Psaume. Dieu de ma louange, ne te tais point!
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
Car ils ouvrent contre moi une bouche méchante et trompeuse, Ils me parlent avec une langue mensongère,
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
Ils m’environnent de discours haineux Et ils me font la guerre sans cause.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
Tandis que je les aime, ils sont mes adversaires; Mais moi je recours à la prière.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
Ils me rendent le mal pour le bien, Et de la haine pour mon amour.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Place-le sous l’autorité d’un méchant, Et qu’un accusateur se tienne à sa droite!
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
Quand on le jugera, qu’il soit déclaré coupable, Et que sa prière passe pour un péché!
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Que ses jours soient peu nombreux, Qu’un autre prenne sa charge!
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Que ses enfants deviennent orphelins, Et sa femme veuve!
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Que ses enfants soient vagabonds et qu’ils mendient, Qu’ils cherchent du pain loin de leur demeure en ruines!
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Que le créancier s’empare de tout ce qui est à lui, Et que les étrangers pillent le fruit de son travail!
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Que nul ne conserve pour lui de l’affection, Et que personne n’ait pitié de ses orphelins!
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Que ses descendants soient exterminés, Et que leur nom s’éteigne dans la génération suivante!
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Que l’iniquité de ses pères reste en souvenir devant l’Éternel, Et que le péché de sa mère ne soit point effacé!
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
Qu’ils soient toujours présents devant l’Éternel, Et qu’il retranche de la terre leur mémoire,
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
Parce qu’il ne s’est pas souvenu d’exercer la miséricorde, Parce qu’il a persécuté le malheureux et l’indigent, Jusqu’à faire mourir l’homme au cœur brisé!
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
Il aimait la malédiction: qu’elle tombe sur lui! Il ne se plaisait pas à la bénédiction: qu’elle s’éloigne de lui!
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
Qu’il revête la malédiction comme son vêtement, Qu’elle pénètre comme de l’eau dans son intérieur, Comme de l’huile dans ses os!
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
Qu’elle lui serve de vêtement pour se couvrir, De ceinture dont il soit toujours ceint!
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Tel soit, de la part de l’Éternel, le salaire de mes ennemis, Et de ceux qui parlent méchamment de moi!
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
Et toi, Éternel, Seigneur! Agis en ma faveur à cause de ton nom, Car ta bonté est grande; délivre-moi!
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
Je suis malheureux et indigent, Et mon cœur est blessé au-dedans de moi.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
Je m’en vais comme l’ombre à son déclin, Je suis chassé comme la sauterelle.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
Mes genoux sont affaiblis par le jeûne, Et mon corps est épuisé de maigreur.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
Je suis pour eux un objet d’opprobre; Ils me regardent, et secouent la tête.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Secours-moi, Éternel, mon Dieu! Sauve-moi par ta bonté!
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
Et qu’ils sachent que c’est ta main, Que c’est toi, Éternel, qui l’as fait!
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
S’ils maudissent, toi tu béniras; S’ils se lèvent, ils seront confus, Et ton serviteur se réjouira.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Que mes adversaires revêtent l’ignominie, Qu’ils se couvrent de leur honte comme d’un manteau!
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
Je louerai de ma bouche hautement l’Éternel, Je le célébrerai au milieu de la multitude;
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
Car il se tient à la droite du pauvre, Pour le délivrer de ceux qui le condamnent.

< Zabura 109 >