< Zabura 108 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
Ein Gesang, ein Lied, von David. Aus Herzensgrund, o Gott, will ich jetzt singen und frohlocken
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Erwache, du mein Stolz! Erwache, Harfe du und Zither! Ich singe wach das Morgenrot.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
Ich preise, Herr, Dich bei den Völkern, und ich besinge Dich bei den Nationen,
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
daß Deine Huld bis an den Himmel reicht, bis zu den Wolken Deine Treue.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Erheb Dich, Gott, soweit der Himmel, und Deinen Ruhm, soweit die Erde reicht!
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Daß Deine Lieblinge gerettet werden, mit Deiner Rechten hilf dazu! Erhöre uns! -
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Gott hat in seinem Heiligtum gesprochen: "Ich soll im Siegesjubel Sichem jetzt verteilen, das Sukkot-Tal vermessen.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
Mein würde Gilead, Manasse mein, und meine Hauptwehr Ephraim und Juda wär mein Herrscherstab.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Ich zwänge Moab auch, das Waschbecken, und Edom, mir die Schuhe herzurichten, und über Philistäa triumphierte ich." -
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Wer bringt mich aber jetzt zur festen Stadt? Wer führt mich jetzt nach Edom hin? -
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Bist Du's nicht, Gott, der uns verstößt, der nicht mit unsren Scharen auszieht, Gott?
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Verschaffe Rettung uns aus dieser Not! Denn Menschenhilfe trügt.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
Mit Gott verrichten wir dann Heldentaten; er nur kann unsere Feinde niedertreten.

< Zabura 108 >