< Zabura 108 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
Een lied, een psalm van David. O God! mijn hart is bereid; ik zal zingen en psalmzingen, ook mijn eer.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Waak op, gij luit en harp! ik zal in den dageraad opwaken.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
Ik zal U loven onder de volken, o HEERE! en ik zal U psalmzingen onder de natien.
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
Want Uw goedertierenheid is groot tot boven de hemelen, en Uw waarheid tot aan de bovenste wolken.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Verhef U, o God! boven de hemelen, en Uw eer over de ganse aarde.
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Opdat Uw beminden bevrijd worden; geef heil door Uw rechterhand, en verhoor ons.
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
God heeft gesproken in Zijn heiligdom, dies zal ik van vreugde opspringen; ik zal Sichem delen, en het dal van Sukkoth zal ik afmeten.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
Gilead is mijn, Manasse is mijn, en Efraim is de sterkte mijns hoofds; Juda is mijn wetgever.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab is mijn waspot; op Edom zal ik mijn schoen werpen; over Palestina zal ik juichen.
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Wie zal mij voeren in een vaste stad? Wie zal mij leiden tot in Edom?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Zult Gij het niet zijn, o God! Die ons verstoten hadt, en Die niet uittoogt, o God! met onze heirkrachten?
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Geef Gij ons hulp uit de benauwdheid; want des mensen heil is ijdelheid.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
In God zullen wij kloeke daden doen, en Hij zal onze wederpartijders vertreden.

< Zabura 108 >