< Zabura 107 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Rendez grâce à Yahvé, car il est bon, car sa bonté est éternelle.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Que les rachetés par Yahvé le disent, qu'il a racheté de la main de l'adversaire,
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
et rassemblés hors des terres, de l'est et de l'ouest, du nord et du sud.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
Ils erraient dans le désert, sur un chemin désert. Ils n'ont pas trouvé de ville où vivre.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Affamé et assoiffé, leur âme s'est évanouie en eux.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Et ils crièrent à Yahvé dans leur détresse, et il les a délivrés de leurs détresses.
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
Il les a aussi conduits par un chemin droit, pour qu'ils puissent aller vivre dans une ville.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Qu'ils louent Yahvé pour sa bonté, pour ses actes merveilleux envers les enfants des hommes!
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
Car il rassasie l'âme languissante. Il remplit de bien l'âme affamée.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Certains se sont assis dans les ténèbres et dans l'ombre de la mort, étant lié par l'affliction et le fer,
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
parce qu'ils se sont rebellés contre les paroles de Dieu, et a condamné le conseil du Très-Haut.
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
C'est pourquoi il a abattu leur cœur par le travail. Ils sont tombés, et il n'y avait personne pour les aider.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Et ils crièrent à Yahvé dans leur détresse, et il les a sauvés de leur détresse.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
Il les a fait sortir des ténèbres et de l'ombre de la mort, et a brisé leurs chaînes.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Qu'ils louent Yahvé pour sa bonté, pour ses actes merveilleux envers les enfants des hommes!
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
Car il a brisé les portes d'airain, et de couper des barres de fer.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Les fous sont affligés à cause de leur désobéissance, et à cause de leurs iniquités.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Leur âme a en horreur toute sorte de nourriture. Ils s'approchent des portes de la mort.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Puis ils crient à Yahvé dans leur détresse, et il les sauve de leurs détresses.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
Il envoie sa parole, et il les guérit, et les délivre de leurs tombes.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Qu'ils louent Yahvé pour sa bonté, pour ses actes merveilleux envers les enfants des hommes!
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
Qu'ils offrent les sacrifices d'actions de grâces, et publier ses exploits en chantant.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
Ceux qui descendent à la mer dans des bateaux, qui font des affaires dans les grandes eaux,
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
ceux-ci voient les actes de Yahvé, et ses merveilles dans les profondeurs.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
Car il commande, et il soulève le vent de la tempête, qui soulève ses vagues.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
Ils montent jusqu'au ciel, ils redescendent dans les profondeurs. Leur âme fond à cause des problèmes.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
Ils titubent d'avant en arrière, et titubent comme un homme ivre, et sont à bout de nerfs.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Alors ils crient à Yahvé dans leur détresse, et il les fait sortir de leur détresse.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
Il fait de la tempête un calme, pour que ses ondes soient immobiles.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Alors ils se réjouissent parce que c'est calme, alors il les amène à l'endroit désiré.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Qu'ils louent Yahvé pour sa bonté, pour ses actions merveilleuses en faveur des enfants des hommes!
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Qu'ils l'exaltent aussi dans l'assemblée du peuple, et le louent sur le siège des anciens.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
Il transforme les fleuves en désert, l'eau jaillit dans une terre assoiffée,
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
et une terre fertile en un désert de sel, à cause de la méchanceté de ceux qui l'habitent.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
Il transforme le désert en une mare d'eau, et une terre aride en sources d'eau.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
Là, il fait vivre les affamés, afin qu'ils puissent préparer une ville pour y vivre,
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
semer des champs, planter des vignes, et récolter les fruits de l'augmentation.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
Il les bénit aussi, de sorte qu'ils se multiplient considérablement. Il ne permet pas à leur bétail de diminuer.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Encore une fois, ils sont diminués et courbés. à travers l'oppression, l'ennui et le chagrin.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
Il déverse le mépris sur les princes, et les fait errer dans un désert sans piste.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
Et pourtant, il sort les nécessiteux de leur détresse, et augmentent leurs familles comme un troupeau.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
Les hommes droits la verront et se réjouiront. Tous les méchants fermeront leur bouche.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Celui qui est sage fera attention à ces choses. Ils considéreront les bontés de Yahvé.

< Zabura 107 >