< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Msifuni Bwana. Mshukuruni Bwana, kwa kuwa ni mwema; upendo wake wadumu milele.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Ni nani awezaye kusimulia matendo makuu ya Bwana au kutangaza kikamilifu sifa zake?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Heri wale wanaodumisha haki, ambao daima wanafanya yaliyo mema.
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Ee Bwana, unikumbuke unapowatendea mema watu wako, uwe msaada wangu unapowaokoa,
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
ili niweze kufurahia mafanikio ya wateule wako, niweze kushiriki katika furaha ya taifa lako, na kuungana na urithi wako katika kukusifu.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Tumetenda dhambi, kama vile baba zetu walivyotenda, tumekosa na tumetenda uovu.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Wakati baba zetu walipokuwa Misri, hawakuzingatia maajabu yako, wala hawakukumbuka wingi wa fadhili zako, bali waliasi kando ya bahari, Bahari ya Shamu.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Hata hivyo aliwaokoa kwa ajili ya jina lake, ili apate kudhihirisha uweza wake mkuu.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Alikemea Bahari ya Shamu, nayo ikakauka, akawaongoza katika vilindi vyake kama vile jangwani.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Aliwaokoa mikononi mwa adui; kutoka mikononi mwa adui aliwakomboa.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Maji yaliwafunika adui zao, hakunusurika hata mmoja.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Ndipo walipoamini ahadi zake, nao wakaimba sifa zake.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Lakini mara walisahau aliyowatendea, wala hawakungojea shauri lake.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Jangwani walitawaliwa na tamaa zao, walimjaribu Mungu nyikani.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Kwa hiyo aliwapa kile walichoomba, lakini akatuma juu yao ugonjwa wa kudhoofisha.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Kambini walimwonea wivu Mose, na pia Aroni aliyekuwa amewekwa wakfu kwa Bwana.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Ardhi ilifunguka ikawameza Dathani, ikawazika Abiramu na kundi lake.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Moto uliwaka katikati ya wafuasi wao, mwali wa moto uliwateketeza waovu.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Huko Horebu walitengeneza ndama, na kuabudu sanamu ya kusubu kwa chuma.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Waliubadilisha Utukufu wao kwa sanamu ya fahali, ambaye hula majani.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Walimsahau Mungu aliyewaokoa, aliyekuwa ametenda mambo makuu huko Misri,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
miujiza katika nchi ya Hamu na mambo ya kutisha huko Bahari ya Shamu.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Kwa hiyo alisema kwamba angewaangamiza: kama Mose mteule wake, asingesimama kati yao na Mungu kuizuia ghadhabu yake kuwaangamiza.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Kisha waliidharau ile nchi nzuri, hawakuiamini ahadi yake.
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
Walinungʼunika ndani ya mahema yao, wala hawakumtii Bwana.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Kwa hiyo akaapa kwa mkono ulioinuliwa kwamba atawafanya waanguke jangwani,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
kuwatawanya wazao wao waanguke miongoni mwa mataifa, na kuwatawanya katika nchi zote.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Walijifunga nira na Baali wa Peori, wakala dhabihu zilizotolewa kwa miungu isiyo na uhai.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Waliichochea hasira ya Bwana, wakamkasirisha kwa matendo yao maovu, nayo tauni ikazuka katikati yao.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Lakini Finehasi alisimama na kuingilia kati, nayo tauni ikazuiliwa.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Hili likahesabiwa kwake haki, kwa vizazi visivyo na mwisho vijavyo.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Kwenye maji ya Meriba, walimkasirisha Bwana, janga likampata Mose kwa sababu yao;
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
kwa maana walimwasi Roho wa Mungu, na maneno yasiyofaa yakatoka midomoni kwa Mose.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Hawakuyaangamiza yale mataifa kama Bwana alivyowaagiza,
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
bali walijichanganya na mataifa na wakazikubali desturi zao.
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Waliabudu sanamu zao, zikawa mtego kwao.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Wakawatoa wana wao na binti zao dhabihu kwa mashetani.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
Walimwaga damu isiyo na hatia, damu za wana wao na binti zao, ambao waliwatoa dhabihu kwa sanamu za Kanaani, nayo nchi ikanajisika kwa damu zao.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Wakajinajisi wenyewe kwa yale waliyotenda; kwa matendo yao wenyewe wakajifanyia ukahaba.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Kwa hiyo Bwana akawakasirikia watu wake na akauchukia sana urithi wake.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Akawakabidhi kwa mataifa na adui zao wakawatawala.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Adui zao wakawaonea na kuwatia chini ya mamlaka yao.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Mara nyingi aliwaokoa lakini walikuwa wamezama kwenye uasi, nao wakajiharibu katika dhambi zao.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Lakini akaangalia mateso yao wakati aliposikia kilio chao;
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
kwa ajili yao akakumbuka agano lake, na kutokana na upendo wake mkuu akapooza hasira yake.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Akawafanya wahurumiwe na wote waliowashikilia mateka.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Ee Bwana Mungu wetu, tuokoe. Tukusanye tena kutoka kwa mataifa, ili tuweze kulishukuru jina lako takatifu, na kushangilia katika sifa zako.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Atukuzwe Bwana, Mungu wa Israeli, tangu milele na hata milele. Watu wote na waseme, “Amen!” Msifuni Bwana.

< Zabura 106 >