< Zabura 104 >

1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Kaksakin LEUM GOD, O ngunik. O LEUM GOD luk, kom fulatlana! Kom nuknukyang ke sunak ac wolana.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Kom afinkomi ke kalem. Kom laknelik kusrao oana sie lohm nuknuk,
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Ac musaela nien muta fulat lom fin kof uh lucng liki kusrao. Kom orekmakin pukunyeng uh oana chariot nutum Ac kasrusr fin eng uh.
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
Kom oru tuh eng uh in mwe utuk kas lom, Ac sarmelik lun sarom uh oana mwet kulansap lom.
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
Kom oakiya faclu fin pwelung ku la — Ac fah tiana mukuikui.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
Kom filiya meoa uh fac oana sie nuknuk, Ac kof uh afinya eol uh.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
Ke kai lom, kof uh kaingelik, Ac ke pusren sap lom, elos sa na kaing.
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
Kof uh sororla fineol uh me nu infahlfal uh, Nu yen kom orala nu selos.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
Kom oakiya sie masrol ma elos tia ku in alukela, Tuh elos in tia sifil afinya faclu.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
Kom oru tuh infacl srisrik in sororma infahlfal uh, Ac infacl lulap in ut inmasrlon inging uh.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
Kof inge orala mwe nim nimen kosro nukewa inimae, Ac kosro donkey nimnim we ac tila malu.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
Won yen engyeng uh elos oru ahng lalos Ac on ulun sak sisken infacl.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
Kom supwama af inkusrao me nu fineol uh, Ac faclu sessesla ke mwe insewowo sum me.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
Kom akkapye mah nu sin cow uh, Ac sacn nu sin mwet uh Tuh elos in yukwiya ac konauk mongo nalos kac,
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
Ac in orala wain in akenganyalos, Ac oil in olive tuh in mwe akmusra, Ac mwe mongo in sang ku nu sin mwet.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
Yokna af in aksroksrokye sak cedar ke inging Lebanon — Sak sunun LEUM GOD, ma El sifacna yukwiya.
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
Won elos orek ahng lalos olo, Won stork elos oru ahng lalos ulun sak fir.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
Nani lemnak elos muta fineol fulat, Ac kosro coney elos wikwik ye fulu uh.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
Kom orala tuh malem uh in mwe akilen kais sie malem; Ac faht uh etu na pacl in tili la.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Kom orala fong, na ke pacl lohsr Kosro lemnak ac oatume.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
Lion fusr elos ngutngut ke elos forfor In suk ma nalos su God El akoo nu selos.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
Na ke faht uh takak, elos ac folokla Ac ona ke luf lalos.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Mwet uh ac som nu ke orekma lalos Ac elos ac orekma nwe ke ekela.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
LEUM GOD, puslana ma kom orala! Ke lalmwetmet lom kom orala ma inge nukewa! Faclu sessesla ke ma kom orala.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Meoa uh pa ingo, yohk ac sralap, Yen kain in ma moul puspis muta we — Kewana ma yohk ac ma srihk.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
Oak palang uh kasrusr fac, Ac Leviathan, wet lulap soko ma kom orala, el srital we.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
Ma inge nukewa elos filiya lulalfongi lalos in kom Tuh kom fah sang mwe mongo nalos ke pacl fal.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Kom sang ma nalos ac elos mongo kac, Kom kitalos ac elos kihpkin.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
Ke pacl kom ngetla lukelos, elos sangeng; Ke kom tulokinya momong lom lukelos, elos misa Ac folokla nu ke kutkut ma elos orekla kac.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Tuh ke kom sang ngunum, elos orekla ma moul; Kom sang moul sasu nu fin fohk uh.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
Lela wolana lun LEUM GOD in oan ma pahtpat! Lela tuh LEUM GOD Elan engan ke ma El orala!
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
El ngetang nu ke faclu, na faclu rarrar; El kahlye fineol uh, na fosryak.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
Nga fah on nu sin LEUM GOD ke moul luk nufon; Nga fah onkakin on in kaksak nu sin God luk ke lusenna moul luk.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Finsrak tuh on luk in mwe akinsewowoyal, Mweyen engan luk tuku sel me.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Lela tuh mwet koluk in kunausyukla liki faclu. Lela elos in wanginla nwe tok. Kaksakin LEUM GOD, O ngunik! Kaksakin LEUM GOD!

< Zabura 104 >