< Zabura 104 >
1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Psaume de David. O mon âme, bénis le Seigneur; Seigneur, ô mon Dieu, tu es très grand, tu es revêtu de gloire et de beauté.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Tu es enveloppé de lumière comme d'un manteau; tu as tendu le ciel comme un tabernacle.
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Il a fait des eaux le toit de ses plus hautes demeures; il a posé les nuées pour être son char; il marche sur les ailes des vents.
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
Des esprits il fait ses anges, et ses serviteurs sont un feu ardent.
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
Il fonde la terre sur son axe; elle ne déviera pas dans les siècles des siècles.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
L'abîme, comme un vêtement, est son manteau, et les eaux s'arrêteront au- dessus des montagnes.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
Elles s'enfuiront, Seigneur, à tes reproches; elles auront peur, à la voix de ton tonnerre.
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
Les montagnes sont montées et les plaines sont descendues au lieu que tu leur avais marqué.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
Tu as posé des limites que les eaux ne passeront pas; elles ne reviendront plus couvrir la terre.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
Le Seigneur a fait jaillir des sources dans les vallées; les eaux couleront entre les montagnes.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
Elles abreuveront toutes les bêtes fauves des champs; les onagres les chercheront pour apaiser leur soif.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
Au-dessus d'elles, les oiseaux du ciel feront leur nid; ils feront entendre leur chant du milieu des rochers.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
Des lieux supérieurs, Dieu arrose les monts; la terre se rassasiera, Seigneur, du fruit de tes œuvres.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
Tu fais pousser l'herbe pour le bétail, et le fourrage pour le service des hommes, afin qu'ils en fassent sortir le blé de la terre.
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
Et le vin réjouit le cœur de l'homme; l'huile égaie son visage; le pain fortifie son cœur.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
Les arbres des champs seront nourris de ces pluies, ainsi que les cèdres du Liban, qu'il a plantés.
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
C'est là que les passereaux feront leur nid, et la famille du héron, qui les surpasse de la tête.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
Les hauteurs des monts seront la demeure des cerfs, et les rochers l'asile du hérisson.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
Dieu a créé la lune pour marquer le temps; le soleil sait où il doit se coucher.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Tu as fait les ténèbres, et la nuit est venue; c'est l'heure où toutes les bêtes fauves traversent la forêt.
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
Les lionceaux rugissent après leur proie, et cherchent les aliments que Dieu leur a donnés.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
Mais le soleil se lève; et ils se réunissent, et ils vont dormir dans leur antre.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Et l'homme s'en va à son travail, et il travaille jusqu'au soir.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
Que tes œuvres sont grandes, Seigneur; tu as fait toutes choses avec sagesse; la terre est pleine de tes créatures.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
La mer est profonde et spacieuse; des reptiles sans nombre y nagent, les petits avec les grands.
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
Des navires la sillonnent; et le dragon formé par vous, vient s'y jouer.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
Tous espèrent en toi, pour que tu leur donne la nourriture au temps opportun.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Tu la leur donne, et ils la recueillent; tu ouvre la main, et ils sont tous remplis des dons de ta bonté.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
Détournes-tu le visage, ils sont troublés; si tu leur ôtes le souffle, ils défailliront et retourneront à leur poussière.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Et si tu envoies ton Esprit, ils seront créés, et tu renouvelleras la face de la terre.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
Que la gloire du Seigneur soit éternelle; le Seigneur se complaira dans ses œuvres.
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
Il regarde la terre, et la fait trembler; il touche les monts, et ils fument.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
Je chanterai le Seigneur toute ma vie; je chanterai mes psaumes à Dieu, tant que j'existerai.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Puisse ma voix lui être douce, et moi je me réjouirai dans le Seigneur.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Puissent les pécheurs et les méchants défaillir sur la terre, et qu'ils ne soient plus! mon âme, bénis le Seigneur!