< Zabura 102 >
1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Yahweh, listen to what I am praying; hear me while I cry out to you!
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Do not (turn away/hide yourself) from me when I (have troubles/am distressed)! Listen to me, and answer me quickly now, when I am calling out to you!
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
My life is ending, like smoke that disappears [SIM]; I have [a high fever which] burns my body like a fire burns [SIM].
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
[I feel like] I am drying up like grass [SIM] that has been beaten/trampled down, and I no longer have a desire to eat food.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
I groan loudly, and my bones can be seen under my skin [because I have become very thin].
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
I am like a [lonely and despised] vulture in the desert, like an owl by itself in the abandoned ruins [of a building/city].
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
I lie awake [at night]; [because there is no one to comfort me], I am like a lonely bird [sitting] on a housetop [SIM].
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
All during the day my enemies insult me; those who make fun of me mention my name [and say, “May you be like him”] when they curse people.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
Because you are very angry [DOU] with me, now [I sit in] ashes [while I am suffering greatly]; and those ashes [fall on] the bread/food that I eat, and what I drink has my tears mixed with it. [It is as though] you have picked me up and thrown me away!
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
My time to remain alive is like an evening shadow [that will soon be gone] [SIM]. I am withering like grass withers [in the hot sun].
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
But Yahweh, you are our king who rules [MTY] forever; people who are not yet born will remember you.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
You will arise and be merciful to [the people of] [MTY] Jerusalem; it is now time for you to do that; this is the time for you to be kind to them.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
Even though (the city has been destroyed/our enemies have destroyed our city), we who serve you still love the stones that [were formerly] in the city walls; because now there is rubble everywhere, we, your people, are very sad when we see it.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Yahweh, [some day the people of other] nations will revere you [MTY]; all the kings on earth will see that you are very glorious/great.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
You will rebuild Jerusalem, and you will appear there with your glory/brightness.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
You will listen to the prayers of your people who are homeless, and you will (not ignore them/do what they request) [LIT] when they plead with you to help them.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Yahweh, [I want to] write these words in order that people in future years [will know what] you have done, in order that people who are not born yet will praise you.
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
They will know that you looked down from your holy/sacred place in heaven [DOU] and saw [what was happening on] the earth.
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
They will know that you hear prisoners groaning and that you will set free those who have been told, “You will be executed.”
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
As a result, people in Jerusalem will praise you [DOU] for what you [have done]
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
when many people [from other people-groups] and [those who are citizens of other] kingdoms gather to worship you.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
[But now] you have caused me to become weak while I am still young; [I think that] I will (not live much longer/ very long/soon die).
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
I say to you, “My God, do not cause me to die now, before I become old! You live forever!
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
You created the world long ago, and you made (the heavens/everything in the sky) with your own hands.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
The earth and the heavens/sky will disappear, but you will remain. They will wear out like clothes wear out. You will get rid of them like [people get rid of] old clothes, and they will no longer exist,
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
but you are [not like the things that you created], [because you are] always the same; you never die.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
[Some day] our children will live safely [in Jerusalem], and their descendants will be protected in your presence.”