< Zabura 102 >

1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Hear my prayer, O Yhwh, and let my cry come unto thee.
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Hide not thy face from me in the day when I am in trouble; incline thine ear unto me: in the day when I call answer me speedily.
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
For my days are consumed like smoke, and my bones are burned as an hearth.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
My heart is smitten, and withered like grass; so that I forget to eat my bread.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
By reason of the voice of my groaning my bones cleave to my skin.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
I am like a pelican of the wilderness: I am like an owl of the desert.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
I watch, and am as a sparrow alone upon the house top.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Mine enemies reproach me all the day; and they that are mad against me are sworn against me.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
For I have eaten ashes like bread, and mingled my drink with weeping,
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
Because of thine indignation and thy wrath: for thou hast lifted me up, and cast me down.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
My days are like a shadow that declineth; and I am withered like grass.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
But thou, O Yhwh, shalt endure for ever; and thy remembrance unto all generations.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Thou shalt arise, and have mercy upon Zion: for the time to favour her, yea, the set time, is come.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
For thy servants take pleasure in her stones, and favour the dust thereof.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
So the heathen shall fear the name of Yhwh, and all the kings of the earth thy glory.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
When Yhwh shall build up Zion, he shall appear in his glory.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
He will regard the prayer of the destitute, and not despise their prayer.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
This shall be written for the generation to come: and the people which shall be created shall praise Yah.
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
For he hath looked down from the height of his sanctuary; from heaven did Yhwh behold the earth;
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
To hear the groaning of the prisoner; to loose those that are appointed to death;
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
To declare the name of Yhwh in Zion, and his praise in Jerusalem;
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
When the people are gathered together, and the kingdoms, to serve Yhwh.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
He weakened my strength in the way; he shortened my days.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
I said, O my God, take me not away in the midst of my days: thy years are throughout all generations.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Of old hast thou laid the foundation of the earth: and the heavens are the work of thy hands.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
They shall perish, but thou shalt endure: yea, all of them shall wax old like a garment; as a vesture shalt thou change them, and they shall be changed:
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
But thou art the same, and thy years shall have no end.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
The children of thy servants shall continue, and their seed shall be established before thee.

< Zabura 102 >