< Zabura 1 >

1 Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
Blessed is the man who walks not in the counsel of the wicked, nor stands in the way of sinners, nor sits in the seat of scoffers,
2 Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
but his delight is in the law of Jehovah, and on his law he meditates day and night.
3 Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
And he shall be like a tree planted by the streams of water, that brings forth its fruit in its season, whose leaf also does not wither. And whatever he does shall prosper.
4 Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
The wicked are not so, but are like the chaff which the wind drives away.
5 Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
Therefore the wicked shall not stand in the judgment, nor sinners in the congregation of the righteous.
6 Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.
For Jehovah knows the way of the righteous, but the way of the wicked shall perish.

< Zabura 1 >