< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
[Parabolæ Salomonis, filii David, regis Israël,
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
ad sciendam sapientiam et disciplinam;
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
ad intelligenda verba prudentiæ, et suscipiendam eruditionem doctrinæ, justitiam, et judicium, et æquitatem:
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
ut detur parvulis astutia, adolescenti scientia et intellectus.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
Audiens sapiens, sapientior erit, et intelligens gubernacula possidebit.
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
Animadvertet parabolam et interpretationem, verba sapientum et ænigmata eorum.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
Timor Domini principium sapientiæ; sapientiam atque doctrinam stulti despiciunt.]
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
[Audi, fili mi, disciplinam patris tui, et ne dimittas legem matris tuæ:
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
ut addatur gratia capiti tuo, et torques collo tuo.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Fili mi, si te lactaverint peccatores, ne acquiescas eis.
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
Si dixerint: Veni nobiscum, insidiemur sanguini; abscondamus tendiculas contra insontem frustra;
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
deglutiamus eum sicut infernus viventem, et integrum quasi descendentem in lacum; (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
omnem pretiosam substantiam reperiemus; implebimus domos nostras spoliis:
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
sortem mitte nobiscum, marsupium unum sit omnium nostrum:
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
fili mi, ne ambules cum eis; prohibe pedem tuum a semitis eorum:
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
pedes enim illorum ad malum currunt, et festinant ut effundant sanguinem.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Frustra autem jacitur rete ante oculos pennatorum.
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
Ipsi quoque contra sanguinem suum insidiantur, et moliuntur fraudes contra animas suas.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Sic semitæ omnis avari: animas possidentium rapiunt.]
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
[Sapientia foris prædicat; in plateis dat vocem suam:
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
in capite turbarum clamitat; in foribus portarum urbis profert verba sua, dicens:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
Usquequo, parvuli, diligitis infantiam, et stulti ea quæ sibi sunt noxia cupient, et imprudentes odibunt scientiam?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
convertimini ad correptionem meam. En proferam vobis spiritum meum, et ostendam vobis verba mea.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Quia vocavi, et renuistis; extendi manum meam, et non fuit qui aspiceret:
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
despexistis omne consilium meum, et increpationes meas neglexistis.
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
Ego quoque in interitu vestro ridebo, et subsannabo cum vobis id quod timebatis advenerit.
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
Cum irruerit repentina calamitas, et interitus quasi tempestas ingruerit; quando venerit super vos tribulatio et angustia:
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
tunc invocabunt me, et non exaudiam; mane consurgent, et non invenient me:
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
eo quod exosam habuerint disciplinam, et timorem Domini non susceperint,
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
nec acquieverint consilio meo, et detraxerint universæ correptioni meæ.
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Comedent igitur fructus viæ suæ, suisque consiliis saturabuntur.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
Aversio parvulorum interficiet eos, et prosperitas stultorum perdet illos.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Qui autem me audierit, absque terrore requiescet, et abundantia perfruetur, timore malorum sublato.]

< Karin Magana 1 >