< Karin Magana 8 >
1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
Tu proclameras la Sagesse, afin que la prudence t'obéisse.
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
Car elle se tient sur les cimes des monts; elle est debout au milieu des sentiers.
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
Elle s'assied devant les portes des riches, et à l'entrée des villes; elle chante
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
C'est vous, ô hommes, que j'appelle; j'élève ma voix devant les fils des hommes.
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
Comprenez, innocents, la subtilité; et vous, ignorants, déposez la science en votre cœur.
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Écoutez-moi; car je vais dire des choses saintes, et proférer de mes lèvres la justice.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
Car ma langue va méditer la vérité, et j'ai en abomination les lèvres menteuses.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
Toutes les paroles de ma bouche sont selon la justice; en elles rien d'oblique et de tortueux.
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
Elles sont toutes offertes à ceux qui comprennent, et justes pour ceux qui trouvent la Sagesse.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Recevez l'instruction et non l'argent, et la science plutôt que l'or raffiné.
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
Car la sagesse a plus de prix que les pierres précieuses, et rien de ce que l'on estime de plus précieux ne la vaut.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
Moi, la Sagesse, j'ai demeuré avec le conseil et le savoir; j'ai appelé à moi l'intelligence.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
La crainte du Seigneur hait l'iniquité, et l'insolence, et l'orgueil et les voies des méchants; et moi aussi, je hais les voies tortueuses des méchants.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
C'est à moi le conseil et la fermeté, à moi la prudence, à moi la force.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
Par moi, les rois règnent, et les princes écrivent des jugements équitables.
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
Par moi, les grands sont glorifiés; par moi, les monarques commandent à la terre.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
Moi j'aime ceux qui m'aiment, et ceux qui me cherchent me trouvent.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
De moi dépendent la fortune et la gloire, et les grandes richesses et la justice.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
Mieux vaut recueillir mes fruits que de l'or et des pierres précieuses, et mes rejetons sont meilleurs que l'argent le plus pur.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
Je me promène dans les voies de l'équité, et je reviens par les voies de la justice;
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
pour distribuer à ceux qui m'aiment une part de mes richesses, et remplir de biens leurs trésors. Après vous avoir publié ce qui arrive chaque jour, je vais énumérer les choses qui sont de toute éternité.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
Le Seigneur m'a créé au commencement de Ses voies, pour faire Ses œuvres.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
Il m'a établie avant le temps, au commencement, avant de créer la terre,
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
et avant de créer les abîmes, avant que l'eau jaillit des fontaines.
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Il m'a engendrée avant que les montagnes et les collines fussent affermies.
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
Le Seigneur a fait les champs et les déserts, et les cimes habitées sous le ciel.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
Quand Il a préparé le ciel, j'étais auprès de Lui, et lorsqu'Il a élevé Son trône sur les vents,
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
et lorsqu'en haut Il a donné aux nuées leur cohérence, et aux fontaines qui sont sous le ciel leur équilibre,
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
et lorsqu'Il a affermi les fondements de la terre;
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
j'étais là, près de Lui, disposant tout avec Lui; j'étais là, et Il Se délectait en moi; chaque jour, à tout moment, je me réjouissais de la vue de Son visage;
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
lorsqu'Il S'applaudissait d'avoir achevé la terre, et Se complaisait dans les fils des hommes.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
Maintenant donc, mon fils, écoute-moi:
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Heureux l'homme qui m'écoutera, et le mortel qui gardera mes voies, veillant le jour à mes portes et gardant le seuil de ma demeure.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
Car mes portes sont des portes de vie, et en elles réside la volonté du Seigneur.
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
Ceux qui pèchent contre moi outragent leur âme, et ceux qui me haïssent aiment la mort.