< Karin Magana 7 >

1 Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
Mein Sohn, behalte meine Reden! Bei dir verwahr, was ich dich heiße!
2 Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
Bewahr dir meine Vorschriften, so wirst du leben, und meine Weisung wie den Augapfel!
3 Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
Bind sie an deine Finger! Auf deines Herzens Tafel schreibe sie!
4 Ka faɗa wa hikima, “Ke’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
Zur Weisheit sprich: "Du bist mir Schwester", nenn Einsicht deine Freundin,
5 za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
auf daß sie dich vor einem andere Weib bewahre, vor einer Fremden, die einschmeichelnd redet!
6 A tagar gidana na leƙa ta labule mai rammuka.
Durchs Fenster meines Hauses, durchs Gitter schaute ich hinaus.
7 Sai na gani a cikin marasa azanci, na lura a cikin samari, wani matashi wanda ba shi da hankali.
Da sah ich einen Jüngling bei den noch Unerfahrenen, bemerkte bei den jungen Leuten einen Unvorsichtigen,
8 Yana gangarawa a titi kusa da kusurwarta, yana tafiya a gefen wajen gidanta
der auf der Gasse nahe einer Ecke ging und in der Richtung meines Hauses schritt
9 da magariba, yayinda rana tana fāɗuwa, yayinda duhun dare yana farawa.
in Dämmerung, am Abende des Tags, in stiller Nachtzeit, in der Dunkelheit.
10 Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
Da tritt auf einmal ihm das Weib entgegen im Dirnenanzug mit geschnürter Brust.
11 (Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
Unruhig trieb sie sich herum; zu Hause hatten ihre Füße keine Ruhe.
12 wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
Ein Schritt jetzt auf die Straße und auf den Markt ein Schritt; sie lauerte an jeder Ecke.
13 Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
Jetzt hascht sie ihn, küßt ihn; mit frecher Miene redet sie ihn an:
14 “Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
"Schlachtopfer darzubringen, lag mir ob; ich habe heute mein Gelübde nun entrichtet.
15 Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
Deswegen bin ich ausgegangen, um dich zu suchen. Ich habe dich gefunden.
16 Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
Mit Decken habe ich bedeckt mein Lager, mit buntem Linnen aus Ägypten.
17 Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
Mit Myrrhen habe ich besprengt mein Lager, mit Aloë und Zimtgewürz.
18 Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
So komm! Wir wollen bis zum Morgen an der Liebe uns berauschen, in Liebe uns genießen.
19 Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
Der Mann ist nicht daheim; er zog auf Reisen in die Ferne.
20 Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
Er nahm den Beutel samt dem Gelde mit sich; am Vollmondstag erst kehrt er wieder heim."
21 Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
So bringt sie ihn herum durch ihr verführerisches Reden und reißt ihn fort durch ihre glatten Lippen.
22 Nan take, ya bi ta kamar saniyar da za a kai mayanka, kamar wawa zuwa wurin da za a ba shi horo
Er folgt ihr nach, der Harmlose, gleich einem Stier, den man zur Schlachtbank führt, gleich einem Hund zum Stricke,
23 sai da kibiya ta soki hantarsa, kamar tsuntsun da ya ruga cikin tarko, ba tare da sani zai zama sanadin ransa ba.
gleich einem Hirsch dahin, wo ihm ein Pfeil die Leber spaltet, gleich einem Vogel, der zur Schlinge eilt, und merkt es nicht, daß es sein Leben gilt.
24 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; ku kasa kunne ga abin da nake faɗa.
Nun, Söhne, horcht auf mich! Auf meines Mundes Reden merket!
25 Kada ku bar zuciyarku ta juya zuwa hanyoyinta ko ku kauce zuwa hanyoyinta.
Laß nicht dein Herz zu ihren Wegen biegen! Verirr dich nicht auf ihre Steige!
26 Ta zama sanadin fāɗuwar yawanci; kisan da ta yi ba ta ƙidayuwa.
Denn viel sind der Erschlagenen, die sie gefällt, und viele sind's, die sie gemordet.
27 Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol h7585)
Die Wege, die zu ihrem Hause führen, sind Wege zu der Unterwelt. Sie führen zu des Todes Kammern. (Sheol h7585)

< Karin Magana 7 >