< Karin Magana 28 >

1 Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
Fogem os impios, sem que ninguem os persiga; mas qualquer justo está confiado como o filho do leão.
2 Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
Pela transgressão da terra são muitos os seus principes, mas por homens prudentes e entendidos a sua continuação será prolongada.
3 Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
O homem pobre que opprime aos pobres é como chuva impetuosa, com que ha falta de pão.
4 Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
Os que deixam a lei louvam o impio; porém os que guardam a lei pelejam contra elles.
5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
Os homens maus não entendem o juizo, mas os que buscam ao Senhor entendem tudo.
6 Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
Melhor é o pobre que anda na sua sinceridade do que o perverso de caminhos, ainda que seja rico.
7 Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
O que guarda a lei é filho entendido, mas o companheiro dos comilões envergonha a seu pae.
8 Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
O que augmenta a sua fazenda com usura e onzena, o ajunta para o que se compadece do pobre.
9 In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
O que desvia os seus ouvidos d'ouvir a lei até a sua oração será abominavel.
10 Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
O que faz com que os rectos errem n'um mau caminho elle mesmo cairá na sua cova: mas os bons herdarão o bem.
11 Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
O homem rico é sabio aos seus proprios olhos, mas o pobre que é entendido o esquadrinha.
12 Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
Quando os justos exultam, grande é a gloria; mas quando os impios sobem, os homens se andam escondendo.
13 Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
O que encobre as suas transgressões nunca prosperará, mas o que as confessa e deixa alcançará misericordia.
14 Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
Bemaventurado o homem que continuamente teme: mas o que endurece o seu coração virá a cair no mal.
15 Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
Como leão bramante, e urso faminto, assim é o impio que domina sobre um povo pobre.
16 Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
O principe falto d'intelligencia tambem multiplica as oppressões, mas o que aborrece a avareza prolongará os seus dias.
17 Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
O homem carregado do sangue de qualquer pessoa fugirá até á cova: ninguem o retenha.
18 Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
O que anda sinceramente salvar-se-ha, mas o perverso em seus caminhos cairá logo.
19 Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
O que lavrar a sua terra virá a fartar-se de pão, mas o que segue a ociosos se fartará de pobreza.
20 Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
O homem fiel abundará em bençãos, mas o que se apressa a enriquecer não será innocente.
21 Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
Ter respeito á apparencia de pessoas não é bom, porque até por um bocado de pão prevaricará o homem
22 Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
O que se apressa a enriquecer é homem de mau olho, porém não sabe que ha de vir sobre elle a pobreza.
23 Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
O que reprehende ao homem depois achará mais favor do que aquelle que lisongeia com a lingua.
24 Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
O que rouba a seu pae, ou a sua mãe, e diz: Não ha transgressão; companheiro é do homem dissipador.
25 Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
O altivo d'animo levanta contendas, mas o que confia no Senhor engordará.
26 Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
O que confia no seu coração é insensato, mas o que anda em sabedoria elle escapará.
27 Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
O que dá ao pobre não terá necessidade, mas o que esconde os seus olhos terá muitas maldições.
28 Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.
Quando os impios se elevam, os homens se andam escondendo, mas quando perecem, os justos se multiplicam.

< Karin Magana 28 >