< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Vær ikke misunnelig på onde mennesker, og ha ikke lyst til å være med dem!
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
For deres hjerte tenker bare på å ødelegge, og deres leber taler ulykke.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
Ved visdom bygges et hus, og ved forstand blir det trygget,
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
og ved kunnskap fylles kammerne med all slags kostelig og herlig gods.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
En vis mann er sterk, og en kyndig mann øker sin kraft.
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
Du skal søke veiledning når du fører krig; hvor det er mange rådgivere, er det frelse.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
Visdom er for høi for dåren; i byporten lukker han ikke sin munn op.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
Den som tenker ut onde råd, blir kalt en renkesmed.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
Dårskaps råd er synd, og en spotter er en vederstyggelighet blandt folk.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
Viser du dig motløs på trengselens dag, så er din kraft ringe.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Frels dem som hentes til døden, og hold tilbake dem som føres skjelvende bort til retterstedet!
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
Når du sier: Se, vi visste ikke noget om det, mon da ikke han skjønner det, han som veier hjertene, og han som gir akt på din sjel, mon ikke han vet det og gjengjelder enhver efter hans gjerninger?
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
Et honning, min sønn, for den er god, og fin honning er søt for din gane!
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Akt visdommen like så gagnlig for din sjel! Har du funnet den, så er det en fremtid for dig, og ditt håp skal ikke bli til intet.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Lur ikke som en ugudelig på den rettferdiges bolig, ødelegg ikke hans hjem!
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
For syv ganger faller den rettferdige og står op igjen, men de ugudelige kastes over ende når ulykken kommer.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
Når din fiende faller, må du ikke glede dig, og når han snubler, må ikke ditt hjerte fryde sig,
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
forat ikke Herren skal se det og mislike det, så han vender sin vrede fra ham.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
La ikke din vrede optendes over de onde, bli ikke harm over de ugudelige!
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
For de onde har ingen fremtid, de ugudeliges lampe slukner.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
Frykt Herren, min sønn, og kongen! Med folk som setter sig op mot dem, må du ikke ha noget å gjøre;
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
for ulykken kommer brått over dem, og ødeleggelsen fra dem begge - hvem kjenner den?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
Også disse ordsprog er av vismenn: Dommeren bør ikke gjøre forskjell på folk.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
Den som sier til den skyldige: Du er uskyldig, ham vil folkeslagene forbanne, ham vil folkene ønske ondt over;
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
men dem som straffer ham, skal det gå vel, og lykke og velsignelse skal komme over dem.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
Kyss på leber gir den som svarer med rette ord.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Fullfør din gjerning der ute og gjør den ferdig på marken! Siden kan du bygge ditt hus.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Vær ikke vidne mot din næste uten årsak! Eller skulde du gjøre svik med dine leber?
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Si ikke: Som han har gjort mot mig, således vil jeg gjøre mot ham; jeg vil gjengjelde enhver efter hans gjerninger.
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
Jeg kom gående forbi en lat manns mark, et uforstandig menneskes vingård,
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
og se, den var helt overgrodd med tistler; nesler skjulte dens bunn, og stengjerdet om den var revet ned.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Og jeg, jeg blev det var, jeg gav akt på det; jeg så det og tok lærdom av det:
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Sier du: La mig ennu sove litt, blunde litt, folde mine hender litt og hvile -
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
så kommer armoden over dig som en landstryker, og nøden som en mann med skjold.

< Karin Magana 24 >