< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Ne æmuleris viros malos, nec desideres esse cum eis:
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
quia rapinas meditatur mens eorum, et fraudes labia eorum loquuntur.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
Sapientia ædificabitur domus, et prudentia roborabitur.
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
In doctrina replebuntur cellaria, universa substantia pretiosa et pulcherrima.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
Vir sapiens, fortis est: et vir doctus, robustus et validus.
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
Quia cum dispositione initur bellum: et erit salus ubi multa consilia sunt.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
Excelsa stulto sapientia, in porta non aperiet os suum.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
Qui cogitat mala facere, stultus vocabitur.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
Cogitatio stulti peccatum est: et abominatio hominum detractor.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
Si desperaveris lassus in die angustiæ: imminuetur fortitudo tua.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Erue eos, qui ducuntur ad mortem: et qui trahuntur ad interitum liberare ne cesses.
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
Si dixeris: Vires non suppetunt: qui inspector est cordis, ipse intelligit, et servatorem animæ tuæ nihil fallit, reddetque homini iuxta opera sua.
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
Comede, fili mi, mel, quia bonum est, et favum dulcissimum gutturi tuo:
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Sic et doctrina sapientiæ animæ tuæ: quam cum inveneris, habebis in novissimis spem, et spes tua non peribit.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Ne insidieris, et quæras impietatem in domo iusti, neque vastes requiem eius.
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
Septies enim cadet iustus, et resurget: impii autem corruent in malum.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
Cum ceciderit inimicus tuus, ne gaudeas, et in ruina eius ne exultet cor tuum:
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
ne forte videat Dominus, et displiceat ei, et auferat ab eo iram suam.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Ne contendas cum pessimis, nec æmuleris impios:
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
quoniam non habent futurorum spem mali, et lucerna impiorum extinguetur.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
Time Dominum, fili mi, et regem: et cum detractoribus non commiscearis:
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
quoniam repente consurget perditio eorum: et ruinam utriusque quis novit?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
Hæc quoque sapientibus: Cognoscere personam in iudicio non est bonum.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
Qui dicunt impio: Iustus es: maledicent eis populi, et detestabuntur eos tribus.
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
Qui arguunt eum, laudabuntur: et super ipsos veniet benedictio.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
Labia deosculabitur, qui recta verba respondet.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Præpara foris opus tuum, et diligenter exerce agrum tuum: ut postea ædifices domum tuam.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Ne sis testis frustra contra proximum tuum: nec lactes quemquam labiis tuis.
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Ne dicas: Quomodo fecit mihi, sic faciam ei: reddam unicuique secundum opus suum.
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
Per agrum hominis pigri transivi, et per vineam viri stulti:
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
et ecce totum repleverant urticæ, et operuerant superficiem eius spinæ, et maceria lapidum destructa erat.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Quod cum vidissem, posui in corde meo, et exemplo didici disciplinam.
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Parum, inquam, dormies, modicum dormitabis, pauxillum manus conseres, ut quiescas:
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
et veniet tibi quasi cursor egestas, et mendicitas quasi vir armatus.

< Karin Magana 24 >