< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Seek not to be like evil men, neither desire to be with them:
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
Because their mind studieth robberies, and their lips speak deceits.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
By wisdom the house shall be built, and by prudence it shall be strengthened.
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
By instruction the storerooms shall be filled with all precious and most beautiful wealth.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
A wise man is strong: and a knowing man, stout and valiant.
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
Because war is managed by due ordering: and there shall be safety where there are many counsels.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
Wisdom is too high for a fool, in the gate he shall not open his mouth.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
He that deviseth to do evils, shall be called a fool.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
The thought of a fool is sin: and the detracter is the abomination of men.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
If thou lose hope being weary in the day of distress, thy strength shall be diminished.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Deliver them that are led to death: and those that are drawn to death forbear not to deliver.
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
If thou say: I have not strength enough: he that seeth into the heart, he understandeth, and nothing deceiveth the keeper of thy soul, and he shall render to a man according to his works.
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
Fat honey, my son, because it is good, and the honeycomb most sweet to thy throat:
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
So also is the doctrine of wisdom to thy soul: which when thou hast found, thou shalt have hope in the end, and thy hope shall not perish.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Lie not in wait, nor seek after wickedness in the house of the just, nor spoil his rest.
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
For a just mall shall fall seven times and shall rise again: but the wicked shall fall down into evil.
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
When thy enemy shall fall, be not glad, and in his ruin let not thy heart rejoice:
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
Lest the Lord see, and it displease him, and he turn away his wrath from him.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Contend not with the wicked, nor seek to be like the ungodly:
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
For evil men have no hope of things to come, and the lamp of the wicked shall be put out.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
My son, fear the Lord and the king: and have nothing to do with detracters.
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
For their destruction shall rise suddenly: and who knoweth the ruin of both?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
These things also to the wise: It is not good to have respect to persons in judgment.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
They that say to the wicked man: Thou art just: shall be cursed by the people, and the tribes shall abhor them.
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
They that rebuke him, shall be praised: and a blessing shall come upon them.
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
He shall kiss the lips, who answereth right words.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Prepare thy work without, and diligently till thy ground: that afterward thou mayst build thy house.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Be not witness without cause against thy neighbour: and deceive not any man with thy lips.
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Say not: I will do to him as he hath done to me: I will render to every one according to his work.
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
I passed by the field of the slothful man, and by the vineyard of the foolish man:
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
And behold it was all filled with nettles, and thorns had covered the face thereof, and the stone wall was broken down.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
Which when I had seen, I laid it up in my heart, and by the example I received instruction.
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Thou wilt sleep a little, said I, thou wilt slumber a little, thou wilt fold thy hands a little to rest:
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
And poverty shall come to thee as a runner, and beggary as an armed man.

< Karin Magana 24 >