< Karin Magana 20 >

1 Ruwan inabi mai yin ba’a ne, barasa kuma mai rikici ne; duk wanda suka sa ya kauce marar hikima ne.
Şarap insanı alaycı, içki gürültücü yapar, Onun etkisiyle yoldan sapan bilge değildir.
2 Fushin sarki yana kama da rurin zaki; duk wanda ya sa shi fushi zai rasa ransa.
Kralın öfkesi genç aslanın kükreyişine benzer, Onu kızdıran canından olur.
3 Bangirma ne ga mutum ya guji faɗa, amma kowane wawa yana saurin yin faɗa.
Kavgadan kaçınmak insan için onurdur, Oysa her ahmak tartışmaya hazırdır.
4 Rago ba ya noma a lokacin noma; saboda haka a lokacin girbi ba ya bukata samun kome.
Sonbaharda çift sürmeyen tembel, Hasatta aradığını bulamaz.
5 Manufofin zuciyar mutum zurfafan ruwaye ne, amma mutum mai basira yakan jawo su.
İnsanın niyetleri derin bir kuyunun suları gibidir, Akıllı kişi onları açığa çıkarır.
6 Kowane mutum gani yake shi mai ƙauna marar ƙarewa ne, amma ina? Da ƙyar ka sami amintacce mutum guda.
İnsanların çoğu, “Vefalıyım” der. Ama sadık birini kim bulabilir?
7 Mai adalci kan yi rayuwa marar abin zargi; masu albarka ne’ya’yan da za su biyo bayansa.
Doğru ve dürüst bir babaya Sahip olan çocuklara ne mutlu!
8 Sa’ad da sarki ya zauna kan kujerarsa don yă yi shari’a, yakan ga dukan mugunta da idanunsa.
Yargı kürsüsünde oturan kral, Kötülüğü gözleriyle ayıklar.
9 Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?
Kim, “Yüreğimi pak kıldım, Günahımdan arındım” diyebilir?
10 Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
RAB hileli tartıdan da, hileli ölçüden de tiksinir.
11 Akan san ƙananan yara ta ayyukansu, ana iya sani ko rayuwarsu amintattu ne, mai nagarta.
Çocuk bile eylemleriyle kendini belli eder, Yaptıkları pak ve doğru mu, değil mi, anlaşılır.
12 Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
İşiten kulağı da gören gözü de RAB yaratmıştır.
13 Kada ka so barci in ba haka ba za ka talauce; ka zauna a faɗake za ka kuwa kasance da sauran abinci.
Uykuyu seversen yoksullaşırsın, Uyanık durursan ekmeğin bol olur.
14 “Kai, ya yi tsada, ya yi tsada!” In ji mai saya; sa’ad da ya tafi yana taƙama a kan ya iya ciniki.
Alıcı, “İşe yaramaz, işe yaramaz” der, Ama alıp gittikten sonra aldığıyla övünür.
15 Zinariya akwai ta, lu’ulu’u kuma ga shi a yalwace, amma leɓunan da suke magana da sani suna da wuyan samu kamar duwatsu masu daraja.
Bol bol altının, mücevherin olabilir, Ama bilgi akıtan dudaklar daha değerlidir.
16 A karɓi rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
Tanımadığı birine kefil olanın giysisini al; Bir yabancı için yapıyorsa bunu, Giysisini rehin tut.
17 Abincin da aka samu ta hanyar zamba yakan zama da daɗi, amma mutum zai ƙarasa da baki cike da yashi.
Hileyle kazanılan yiyecek insana tatlı gelir, Ama sonra ağza dolan çakıl gibidir.
18 Ka yi shirye-shirye ta wurin neman shawara; in kana yaƙi, ka sami bishewa.
Tasarılarını danışarak yap, Yöntemlere uyarak savaş.
19 Mai gulma yakan lalace yarda; saboda haka ka guji mutum mai yawan surutu.
Dedikoducu sır saklayamaz, Bu nedenle ağzı gevşek olanla arkadaşlık etme.
20 In mutum ya zargi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, fitilarsa za tă mutu a tsakiyar duhu.
Annesine ya da babasına sövenin Işığı zifiri karanlıkta sönecek.
21 Gādon da aka samu da sauri a farkon farawa ba zai zama mai albarka a ƙarshe ba.
Tez elde edilen mirasın Sonu bereketli olmaz.
22 Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
“Bu kötülüğü sana ödeteceğim” deme; RAB'bi bekle, O seni kurtarır.
23 Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
RAB hileli tartıdan tiksinir, Hileli teraziden hoşlanmaz.
24 Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
İnsanın adımlarını RAB yönlendirir; Öyleyse insan tuttuğu yolu nasıl anlayabilir?
25 Tarko ne ga mutum ya keɓe wani abu da ba tunani daga baya kuma ya yi la’akari da alkawarinsa.
Düşünmeden adakta bulunmak Sakıncalıdır.
26 Sarki mai hikima yakan gane mugunta; ya hukunta su ba tausayi.
Bilge kral kötüleri ayıklar, Harman döver gibi cezalandırır.
27 Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
İnsanın ruhu RAB'bin ışığıdır, İç varlığın derinliklerine işler.
28 Ƙauna da aminci kan kiyaye sarki lafiya; ta wurin ƙauna sarautarsa za tă zauna a kafe.
Sevgi ve sadakat kralın güvencesidir. Onun tahtını sağlamlaştıran sevgidir.
29 Ɗaukakar matasa maza ita ce ƙarfinsu, furfura ita ce darajar tsofaffi.
Gençlerin görkemi güçleri, Yaşlıların onuru ağarmış saçlardır.
30 Naushi da rauni kan share mugunta, dūka kuma kan tsabtacce lamiri.
Yaralayan darbeler kötülüğü temizler, Kötek iç varlığın derinliklerini paklar.

< Karin Magana 20 >