< Karin Magana 19 >

1 Gara matalauci wanda yake marar laifi da wawa wanda leɓunansa masu ƙarya ne.
Better [is] the poor that walketh in his integrity, than [he that is] perverse in his lips, and is a fool.
2 Ba shi da kyau ka kasance da niyya babu sani, ko ka kasance mai garaje ka ɓace hanya.
Also, [that] the soul [be] without knowledge, [it is] not good; and he that hasteth with [his] feet sinneth.
3 Wautar mutum kan lalatar da ransa, duk da haka zuciyarsa kan ba wa Ubangiji laifi.
The foolishness of man perverteth his way: and his heart fretteth against the LORD.
4 Wadata kan kawo abokai da yawa, amma abokin matalauci kan bar shi.
Wealth maketh many friends; but the poor is separated from his neighbour.
5 Mai ba da shaidar ƙarya ba zai tafi babu hukunci ba, kuma duk wanda ya baza ƙarairayi ba zai kuɓuta ba.
A false witness shall not be unpunished, and [he that] speaketh lies shall not escape.
6 Kowa na ƙoƙari ya sami farin jini wurin mai mulki, kuma kowa na so a ce shi abokin mutumin nan mai yawan kyauta ne.
Many will intreat the favour of the prince: and every man [is] a friend to him that giveth gifts.
7 ’Yan’uwan matalauci sukan guje shi, balle abokansa, su ma za su guje shi. Ko da yake matalaucin yana binsu yana roƙo, ba zai sam su ba.
All the brethren of the poor do hate him: how much more do his friends go far from him? he pursueth [them with] words, [yet] they [are] wanting [to him].
8 Duk wanda ya sami hikima yana ƙaunar ransa; duka wanda yake jin daɗi fahimi kan ci gaba.
He that getteth wisdom loveth his own soul: he that keepeth understanding shall find good.
9 Mai shaidar ƙarya ba zai tafi babu hukunci ba, kuma duk mai baza ƙarairayi zai hallaka.
A false witness shall not be unpunished, and [he that] speaketh lies shall perish.
10 Bai dace da wawa ya yi rayuwa cikin jin daɗi ba, haka ya fi muni bawa ya yi mulki a kan sarki!
Delight is not seemly for a fool; much less for a servant to have rule over princes.
11 Hikimar mutum kan ba shi haƙuri; ɗaukakarsa ce ya ƙyale laifi.
The discretion of a man deferreth his anger; and [it is] his glory to pass over a transgression.
12 Fushin sarki yana kama da rurin zaki, amma tagomashinsa yana kama da raba a kan ciyawa.
The king’s wrath [is] as the roaring of a lion; but his favour [is] as dew upon the grass.
13 Wawan yaro lalacin mahaifinsa ne, mace mai yawan faɗa tana kama da ɗiɗɗigar ruwa.
A foolish son [is] the calamity of his father: and the contentions of a wife [are] a continual dropping.
14 Ana gādon dawakai da wadata daga iyaye ne, amma mace mai basira daga Ubangiji ne.
House and riches [are] the inheritance of fathers: and a prudent wife [is] from the LORD.
15 Ragwanci kan jawo zurfin barci, mutum mai sanyin jiki kuma yana tare da yunwa.
Slothfulness casteth into a deep sleep; and an idle soul shall suffer hunger.
16 Duk wanda ya bi umarnai kan tsare ransa, amma duk wanda ya ƙi binsu zai mutu.
He that keepeth the commandment keepeth his own soul; [but] he that despiseth his ways shall die.
17 Duk wanda yake kirki ga matalauta yana ba wa Ubangiji bashi ne, zai kuwa sami lada game da abin da ya yi.
He that hath pity upon the poor lendeth unto the LORD; and that which he hath given will he pay him again.
18 Ka hori ɗanka, gama yin haka akwai sa zuciya; kada ka goyi baya lalacewarsa.
Chasten thy son while there is hope, and let not thy soul spare for his crying.
19 Dole mai zafin rai yă biya tara; in ka fisshe shi sau ɗaya, to, sai ka sāke yin haka.
A man of great wrath shall suffer punishment: for if thou deliver [him], yet thou must do it again.
20 Ka kasa kunne ga shawara ka kuma yarda da umarni, a ƙarshe kuwa za ka yi hikima.
Hear counsel, and receive instruction, that thou mayest be wise in thy latter end.
21 Da yawa ne shirye-shiryen zuciyar mutum, amma manufar Ubangiji ce takan cika.
[There are] many devices in a man’s heart; nevertheless the counsel of the LORD, that shall stand.
22 Abin da mutum yake sha’awa shi ne ƙauna marar ƙarewa; gara ka zama matalauci da ka zama maƙaryaci.
The desire of a man [is] his kindness: and a poor man [is] better than a liar.
23 Tsoron Ubangiji yakan kai ga rai. Sa’an nan mutum ya sami biyan bukata, ba abin da zai cuce shi.
The fear of the LORD [tendeth] to life: and [he that hath it] shall abide satisfied; he shall not be visited with evil.
24 Rago kan sa hannunsa a kwano ba ya ma iya ɗaga shi ya kai bakinsa!
A slothful [man] hideth his hand in [his] bosom, and will not so much as bring it to his mouth again.
25 Ka bulale mai ba’a, marasa azanci kuwa za su yi la’akari; ka tsawata wa mai basira, zai kuwa ƙara sani.
Smite a scorner, and the simple will beware: and reprove one that hath understanding, [and] he will understand knowledge.
26 Duk wanda ya yi wa mahaifinsa fashi ya kuma kori mahaifiyarsa ɗa ne da kan kawo kunya da wulaƙanci.
He that wasteth [his] father, [and] chaseth away [his] mother, [is] a son that causeth shame, and bringeth reproach.
27 In ka daina jin umarni, ɗana, za ka kuwa kauce daga kalmomin sani.
Cease, my son, to hear the instruction [that causeth] to err from the words of knowledge.
28 Mai shaidar da yake malalaci yana wa shari’a ba’a ne, bakin mugaye kuma na haɗiye mugunta.
An ungodly witness scorneth judgment: and the mouth of the wicked devoureth iniquity.
29 An shirya tara saboda masu ba’a ne, dūka kuma saboda bayan wawaye.
Judgments are prepared for scorners, and stripes for the back of fools.

< Karin Magana 19 >