< Karin Magana 11 >

1 Ubangiji yana ƙyamar ma’aunan zamba, amma ma’aunin da suke daidai ne abin farin cikinsa.
RAB hileli teraziden iğrenir, Hilesiz tartıdansa hoşnut kalır.
2 Sa’ad da girman kai ya zo, sai shan kunya ta zo, amma hikima kan zo tare da ƙasƙantar da kai.
Küstahlığın ardından utanç gelir, Ama bilgelik alçakgönüllülerdedir.
3 Mutuncin masu aikata gaskiya takan bi da su, amma marasa aminci sukan hallaka ta wurin cin amanar da suke yi.
Erdemlinin dürüstlüğü ona yol gösterir, Hainin yalancılığıysa yıkıma götürür.
4 Dukiya ba ta da amfani a ranar fushi, amma adalci kan yi ceto daga mutuwa.
Gazap günü servet işe yaramaz, Oysa doğruluk ölümden kurtarır.
5 Adalcin marasa laifi kan miƙe hanyarsu, amma akan ƙasƙantar da mugaye ta wurin muguntarsu.
Dürüst insanın doğruluğu onun yolunu düzler, Kötü kişiyse kötülüğü yüzünden yıkılıp düşer.
6 Adalcin masu aikata gaskiya kan cece su, amma rashin aminci tarko ne ga mugayen sha’awace-sha’awace.
Erdemlinin doğruluğu onu kurtarır, Ama haini kendi hırsı ele verir.
7 Sa’ad da mugu ya mutu, sa zuciyarsa kan hallaka; dukan abin da ya sa zuciya daga ikonsa ba ya amfana kome.
Kötü kişi öldüğünde umutları yok olur, Güvendiği güç de biter.
8 Akan kuɓutar da mai adalci daga wahala, sai ta dawo wa mugu a maimako.
Doğru kişi sıkıntıdan kurtulur, Onun yerine sıkıntıyı kötü kişi çeker.
9 Da bakinsa marar sanin Allah kan hallaka maƙwabcinsa, amma ta wurin sani mai adalci kan kuɓuta.
Tanrısız kişi başkalarını ağzıyla yıkıma götürür, Oysa doğrular bilgi sayesinde kurtulur.
10 Sa’ad da adali ya yi nasara, birnin kan yi farin ciki; sa’ad da mugu ya hallaka, akwai sowa ta farin ciki.
Doğruların başarısına kent bayram eder, Kötülerin ölümüne sevinç çığlıkları atılır.
11 Ta wurin albarkar mai aikata gaskiya birni kan ƙasaita, amma ta wurin bakin mugu akan hallaka birnin.
Dürüstlerin kutsamasıyla kent gelişir, Ama kötülerin ağzı kenti yerle bir eder.
12 Mutum da ba shi da azanci kan ki maƙwabci, amma mutum mai fahimi kan ƙame harshensa.
Başkasını küçük gören sağduyudan yoksundur, Akıllı kişiyse dilini tutar.
13 Gulma yakan lalace yarda, amma mutum mai aminci kan kiyaye asiri.
Dedikoducu sır saklayamaz, Oysa güvenilir insan sırdaş olur.
14 Saboda rashin jagora al’umma takan fāɗi, amma masu ba da shawara da yawa kan tabbatar da nasara.
Yol göstereni olmayan ulus düşer, Danışmanı bol olan zafere gider.
15 Duk wanda ya ɗauki lamunin wani tabbatacce zai sha wahala, amma duk wanda ya ƙi ya sa hannu a ɗaukar lamuni ba ruwansa.
Yabancıya kefil olan mutlaka zarar görür, Kefaletten kaçınan güvenlik içinde yaşar.
16 Mace mai hankali na samu bangirma, amma azzalumai za su sami dukiya.
Sevecen kadın onur, Zorbalarsa yalnızca servet kazanır.
17 Mutumin kirki kan ribance kansa, amma mugu kan kawo wa kansa wahala.
İyilikseverin yararı kendinedir, Gaddarsa kendi başına bela getirir.
18 Mugun mutum kan sami albashin ƙarya amma shi da ya shuka adalci zai girbe lada tabbatacce.
Kötü kişinin kazancı aldatıcıdır, Doğruluk ekenin ödülüyse güvenlidir.
19 Mutum mai adalci da gaske yakan sami rai, amma shi da ya duƙufa ga aikata mugunta kan tarar da mutuwarsa.
Yürekten doğru olan yaşama kavuşur, Kötülüğün ardından giden ölümünü hazırlar.
20 Ubangiji yana ƙyamar mutane masu muguwar zuciya amma yana jin daɗin waɗanda hanyoyinsu ba su da laifi.
RAB sapık yürekliden iğrenir, Dürüst yaşayandan hoşnut kalır.
21 Ka tabbata da wannan. Mugaye ba za su tafi babu hukunci ba, amma waɗanda suke masu adalci za su tafi babu hukunci.
Bilin ki, kötü kişi cezasız kalmaz, Doğruların soyuysa kurtulur.
22 Kamar zinariya a hancin alade haka kyan mace wadda ba ta da hankali.
Sağduyudan yoksun kadının güzelliği, Domuzun burnundaki altın halkaya benzer.
23 Sha’awar adalai kan ƙare kawai a aikata alheri, amma sa zuciyar mugaye kan ƙarasa kawai a fushi.
Doğruların isteği hep iyilikle sonuçlanır, Kötülerin umutlarıysa gazapla.
24 Wani mutum kan bayar hannu sake, duk da haka yakan sami fiye; wani yakan riƙe abin da ba nasa ba, amma sai ya ƙarasa cikin talauci.
Eliaçık olan daha çok kazanır, Hak yiyenin sonuysa yoksulluktur.
25 Mutum mai kyauta zai azurta; shi da yakan taimake waɗansu, za a taimake shi.
Cömert olan bolluğa erecek, Başkasına su verene su verilecek.
26 Mutane kan la’anci mai ɓoye hatsi yana jira ya yi tsada, amma albarka kan zauna a kan wanda yake niyya ya sayar.
Halk buğday istifleyeni lanetler, Ama buğday satanı kutsar.
27 Duk mai nema alheri kan sami alheri, amma mugu kan zo wa wanda yake nemansa.
İyiliği amaç edinen beğeni kazanır, Kötülüğü amaç edinense kötülüğe uğrar.
28 Duk wanda ya dogara ga arzikinsa zai fāɗi, amma adali zai yi nasara kamar koren ganye.
Zenginliğine güvenen tepetaklak gidecek, Oysa doğrular dalındaki yaprak gibi gelişecek.
29 Duk wanda ya kawo wahala wa iyalinsa zai gāji iska kawai, kuma wawa zai zama bawan masu hikima.
Ailesine sıkıntı çektirenin mirası yeldir, Ahmaklar da bilgelerin kulu olur.
30 ’Ya’yan itacen adali itacen rai ne, kuma duk mai samun rayuka mai hikima ne.
Doğru kişinin işleri yaşam ağacının meyvesine benzer, Bilge kişi insanları kazanır.
31 In masu adalci sun sami abin da ya dace da su a duniya, yaya zai zama ga marasa sanin Allah da kuma masu zunubi!
Bu dünyada doğru kişi bile cezalandırılırsa, Kötülerle günahlıların cezalandırılacağı kesindir.

< Karin Magana 11 >