< Ƙidaya 9 >
1 Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
Yahweh spoke to Moses in the wilderness of Sinai, in the first month of the second year after they came out from the land of Egypt. He said,
2 “Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
“Let the people of Israel keep the Passover at its fixed time of year.
3 A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
On the fourteenth day of this month, at evening, you must keep the Passover at its fixed time of year. You must keep it, follow all the regulations, and obey all the decrees that are related to it.”
4 Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
So, Moses told the people of Israel that they should keep the Festival of the Passover.
5 suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
So they kept the Passover in the first month, on the fourteenth day of the month, at evening, in the wilderness of Sinai. The people of Israel obeyed everything that Yahweh commanded Moses to do.
6 Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
There were certain men who became unclean by the body of a dead man. They could not keep the Passover on that day. They went before Moses and Aaron on that same day.
7 suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
Those men said to Moses, “We are unclean because of the dead body of a man. Why do you keep us from offering the sacrifice to Yahweh at the fixed time of year among the people of Israel?”
8 Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
Moses said to them, “Wait for me to hear what Yahweh will instruct about you.”
9 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh spoke to Moses. He said,
10 “Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
“Speak to the people of Israel. Say, 'If any of you or your descendants are unclean because of a dead body, or are on a long journey, he may still keep the Passover to Yahweh.'
11 Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
In the second month on the fourteenth day at evening, they will eat the Passover meal. They must eat the Passover lamb with bread that is made without yeast and with bitter herbs.
12 Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
They must not leave any of it until the morning, or break any of its bones. They must follow all the regulations for the Passover.
13 Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
But any person who is clean and is not on a journey, but who fails to keep the Passover, that person must be cut off from his people because he did not offer the sacrifice that Yahweh requires at the fixed time of year. That man must carry his sin.
14 “‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
If a stranger lives among you and keeps the Passover in Yahweh's honor, he must keep it and do all he commands, keeping the rules of the Passover, and obeying the laws for it. You must have the same law for the foreigner and for all who have been born in the land.”
15 A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
On the day that the tabernacle was set up, the cloud covered the tabernacle, the tent of the covenant decrees. At evening the cloud was over the tabernacle. It appeared like fire until morning.
16 Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
It continued that way. The cloud covered the tabernacle and appeared like fire at night.
17 Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
Whenever the cloud was taken up from over the tent, the people of Israel would set out on their journey. Wherever the cloud stopped, the people would camp.
18 Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
At Yahweh's command, the people of Israel would travel, and at his command, they would camp. While the cloud stopped over the tabernacle, they would stay in their camp.
19 Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
When the cloud remained on the tabernacle for many days, then the people of Israel would obey Yahweh's instructions and not travel.
20 Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
Sometimes the cloud remained a few days on the tabernacle. In that case, they would obey Yahweh's command—they would make camp and then travel on again at his command.
21 Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
Sometimes the cloud was present in camp from evening until morning. When the cloud lifted in the morning, they journeyed. If it continued for a day and for a night, only when the cloud lifted would they journey on.
22 Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
Whether the cloud stayed on the tabernacle for two days, a month, or a year, for as long as it stayed there, the people of Israel would stay in their camp and not travel. But whenever the cloud was taken up, they would set out on their journey.
23 Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.
They would camp at Yahweh's command, and they would travel at his command. They obeyed Yahweh's command given through Moses.