< Ƙidaya 31 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD said to Moses,
2 “Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
“Take vengeance on the Midianites for the Israelites. After that, you will be gathered to your people.”
3 Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
So Moses told the people, “Arm some of your men for war, that they may go against the Midianites and execute the LORD’s vengeance on them.
4 Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
Send into battle a thousand men from each tribe of Israel.”
5 Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
So a thousand men were recruited from each tribe of Israel—twelve thousand armed for war.
6 Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
And Moses sent the thousand from each tribe into battle, along with Phinehas son of Eleazar the priest, who took with him the vessels of the sanctuary and the trumpets for signaling.
7 Suka yi yaƙi da Midiyawa, suka kashe kowane mutum yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Then they waged war against Midian, as the LORD had commanded Moses, and they killed every male.
8 A cikin waɗanda aka kashe kuwa akwai Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba; sarakuna biyar na Mediyawa. Suka kuma kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi.
Among the slain were Evi, Rekem, Zur, Hur, and Reba—the five kings of Midian. They also killed Balaam son of Beor with the sword.
9 Isra’ilawa suka kwashe mata da yaran Midiyawa, a matsayin bayi. Suka kwashe shanunsu da tumakinsu da kuma dukan dukiyarsu, a matsayin ganima.
The Israelites captured the Midianite women and their children, and they plundered all their herds, flocks, and goods.
10 Suka ƙone dukan garuruwan da Midiyawa suke zama, da dukan sansaninsu.
Then they burned all the cities where the Midianites had lived, as well as all their encampments,
11 Suka kwashe dukan ganima haɗe da mutane da dabbobi,
and carried away all the plunder and spoils, both people and animals.
12 suka kawo bayi da ganiman nan, wurin Musa da Eleyazar firist, da kuma jama’ar Isra’ilawa, a sansaninsu a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko.
They brought the captives, spoils, and plunder to Moses, to Eleazar the priest, and to the congregation of Israel at the camp on the plains of Moab, by the Jordan across from Jericho.
13 Musa, da Eleyazar firist da dukan shugabannin jama’a, suka fito suka tarye su a bayan sansani.
And Moses, Eleazar the priest, and all the leaders of the congregation went to meet them outside the camp.
14 Musa kuwa ya husata da shugabannin sojojin da suke shugabannin dubbai da shugabannin ɗari-ɗarin da suka dawo daga yaƙi.
But Moses was angry with the officers of the army—the commanders of thousands and commanders of hundreds—who were returning from the battle.
15 Ya tambaye su ya ce, “Kun bar dukan mata da rai?
“Have you spared all the women?” he asked them.
16 Su ne waɗanda suka bi shawarar Bala’am suka kuma zama sanadin sa Isra’ilawa suka juya wa Ubangiji baya, har ya kawo abin da ya faru da Feyor, har annoba ya kashe dukan mutanen Ubangiji.
“Look, these women caused the sons of Israel, through the counsel of Balaam, to turn unfaithfully against the LORD at Peor, so that the plague struck the congregation of the LORD.
17 Yanzu ku kashe dukan yara maza, ku kuma kashe kowace macen da ta yi lalata da namiji,
So now, kill all the boys, as well as every woman who has had relations with a man,
18 amma ku bar kowace yarinyar da ba tă taɓa yin lalata da namiji ba.
but spare for yourselves every girl who has never had relations with a man.
19 “Dukanku da kuka kashe mutum, ko kuka taɓa wani da aka kashe, dole ku kasance a bayan sansani har kwana bakwai. A rana ta uku da rana ta bakwai dole ku tsabtacce kanku da kuma bayinku.
All of you who have killed a person or touched the dead are to remain outside the camp for seven days. On the third day and the seventh day you are to purify both yourselves and your captives.
20 Ku tsarkake kowace taguwa da kuma kome da aka yi da fata, da gashin akuya, ko kuwa itace.”
And purify every garment and leather good, everything made of goat’s hair, and every article of wood.”
21 Sa’an nan Eleyazar firist, ya ce wa sojojin da suka je yaƙi, “Wannan ita ce ƙa’idar da Ubangiji ya ba wa Musa.
Then Eleazar the priest said to the soldiers who had gone into battle, “This is the statute of the law which the LORD has commanded Moses:
22 Zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, kuza, darma
Only the gold, silver, bronze, iron, tin, and lead—
23 da dukan abin da wuta ba ta iya ci, dole yă shiga wuta sa’an nan zai zama da tsabta. Amma dole a kuma tsarkake ta da ruwan tsarkakewa. Duk abin da wuta za tă iya ci, dole a shigar da ita a ruwan tsarkakewa.
everything that can withstand the fire—must be put through the fire, and it will be clean. But it must still be purified with the water of purification. And everything that cannot withstand the fire must pass through the water.
24 A rana ta bakwai za ku wanke tufafinku, sa’an nan za ku tsarkaka, bayan haka ku shigo sansani.”
On the seventh day you are to wash your clothes, and you will be clean. After that you may enter the camp.”
25 Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
The LORD said to Moses,
26 “Da kai da Eleyazar firist, da shugabannin jama’a, ku ƙidaya dukan mutane da dabbobin da aka ci da yaƙi.
“You and Eleazar the priest and the family heads of the congregation are to take a count of what was captured, both of man and beast.
27 Ku kasa ganimar kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗaya kuma ku ba wa jama’a.
Then divide the captives between the troops who went out to battle and the rest of the congregation.
28 Daga sojojin da suka je yaƙin kuwa, ka ware ganima wa Ubangiji, ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar.
Set aside a tribute for the LORD from what belongs to the soldiers who went into battle: one out of every five hundred, whether persons, cattle, donkeys, or sheep.
29 Ka ɗauki wannan sashe daga rabin rabonsu ka ba wa Eleyazar firist, a matsayin sashe na Ubangiji.
Take it from their half and give it to Eleazar the priest as an offering to the LORD.
30 Daga cikin rabin rabon Isra’ilawa, ka zaɓi ɗaya daga kowane hamsin na mutane, shanu, jakuna, tumaki, awaki ko kuma sauran dabbobi. Ka ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.”
From the Israelites’ half, take one out of every fifty, whether persons, cattle, donkeys, sheep, or other animals, and give them to the Levites who keep charge of the tabernacle of the LORD.”
31 Saboda haka Musa da Eleyazar suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.
So Moses and Eleazar the priest did as the LORD had commanded Moses,
32 Yawan ganimar da sojoji suka kawo ita ce tumaki 675,000
and this plunder remained from the spoils the soldiers had taken: 675,000 sheep,
33 shanu 72,000
72,000 cattle,
34 da jakuna 61,000.
61,000 donkeys,
35 Akwai kuma mata 32,000 da ba su yi lalata ba da namiji ba.
and 32,000 women who had not slept with a man.
36 Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi shi ne, tumaki 337,500,
This was the half portion for those who had gone to war: 337,500 sheep,
37 tumakin da aka ware wa Ubangiji kuwa 657 ne;
including a tribute to the LORD of 675,
38 shanu 36,000, shanun da aka ware wa Ubangiji kuwa 72 ne;
36,000 cattle, including a tribute to the LORD of 72,
39 jakuna 30,500, jakunan da aka ware wa Ubangiji kuwa 61 ne;
30,500 donkeys, including a tribute to the LORD of 61,
40 mutane 16,000, mutanen da aka ware wa Ubangiji kuwa 32 ne.
and 16,000 people, including a tribute to the LORD of 32.
41 Musa ya ba wa Eleyazar abin da aka ware wa Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Moses gave the tribute to Eleazar the priest as an offering for the LORD, as the LORD had commanded Moses.
42 Kashin da aka ba wa Isra’ilawa, wanda Musa ya ware daga cikin na waɗanda suka tafi yaƙi,
From the Israelites’ half, which Moses had set apart from the men who had gone to war,
43 kashin da aka ba wa jama’a kuwa tumaki 337,500 ne,
this half belonged to the congregation: 337,500 sheep,
44 shanu 36,000,
36,000 cattle,
45 jakuna 30,500
30,500 donkeys,
46 da mutane 16,000.
and 16,000 people.
47 Daga rabin kashi na Isra’ilawa, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na mutane da na dabbobi, yadda Ubangiji ya umarce shi, ya ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.
From the Israelites’ half, Moses took one out of every fifty persons and animals and gave them to the Levites who kept charge of the tabernacle of the LORD, as the LORD had commanded him.
48 Sai shugabannin da suka shugabancin rundunar yaƙin, shugabanni na dubu-dubu da shugabanni na ɗari-ɗari, suka zo wurin Musa
Then the officers who were over the units of the army—the commanders of thousands and of hundreds—approached Moses
49 suka ce masa, “Barorinka sun ƙidaya mayaƙan da suke ƙarƙashinmu, babu ko ɗayan ya ɓace.
and said, “Your servants have counted the soldiers under our command, and not one of us is missing.
50 Saboda haka mun kawo wa Ubangiji hadaya na kayan zinariya da kowannenmu ya samu, mundaye, ƙawane,’yan kunne da duwatsun wuya, don yin wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.”
So we have brought to the LORD an offering of the gold articles each man acquired—armlets, bracelets, rings, earrings, and necklaces—to make atonement for ourselves before the LORD.”
51 Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka daga gare su.
So Moses and Eleazar the priest received from them all the articles made out of gold.
52 Dukan zinariya da shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, waɗanda Musa da Eleyazar suka karɓa, suka kuma miƙa hadaya ga Ubangiji, nauyinta ta kai shekel 16,750.
All the gold that the commanders of thousands and of hundreds presented as an offering to the LORD weighed 16,750 shekels.
53 Kowane soja, ya kwashi ganima wa kansa.
Each of the soldiers had taken plunder for himself.
54 Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya daga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, suka kawo cikin Tentin Sujada, don su zama abin tuni ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji.
And Moses and Eleazar the priest received the gold from the commanders of thousands and of hundreds and brought it into the Tent of Meeting as a memorial for the Israelites before the LORD.

< Ƙidaya 31 >