< Ƙidaya 16 >

1 Kora ɗan Izhar, wanda yake Balawe ne daga dangin Kohatawa, wata rana ya nemi Datan da Abiram’ya’yan Eliyab, da On ɗan Felet dukansu daga kabilar Ruben, suka haɗa kai
And Korah, son of Izhar, son of Kohath, son of Levi, takes both Dathan and Abiram sons of Eliab, and On son of Peleth, sons of Reuben,
2 suka tayar wa Musa. Sai suka nemi goyon bayan sanannun shugabannin Isra’ilawa da aka naɗa a majalisa su guda 250,
and they rise up before Moses with men of the sons of Israel, two hundred and fifty princes of the congregation, called of the convention, men of renown,
3 tare kuwa suka zo wurin Musa da Haruna, suka ce musu, “Kun wuce gona da iri! Dukan jama’an nan masu tsarki ne, kowannensu, Ubangiji kuma yana tare da su. Me ya sa kuke ɗaukan kanku fiye da taron jama’ar Ubangiji?”
and they are assembled against Moses and against Aaron, and say to them, “Enough of you! For all the congregation—all of them [are] holy, and YHWH [is] in their midst; and why do you lift yourselves up above the assembly of YHWH?”
4 Da Musa ya ji haka, sai ya fāɗi rubda ciki ya yi addu’a
And Moses hears, and falls on his face,
5 Sai ya ce wa Kora da dukan waɗannan da suke tare shi, “Da safe, Ubangiji zai nuna wane ne yake nasa, da kuma wane ne yake da tsarki. Zai kuma sa mutumin yă zo kusa da shi. Mutumin da ya zaɓa kuwa zai sa yă zo kusa da shi.
and he speaks to Korah and to all his congregation, saying, “Indeed, [in the] morning YHWH may cause [you] to know those who are His and him who is holy, and has brought [him] near to Him; even him whom He fixes on He brings near to Him.
6 Kai Kora da ƙungiyarka, gobe, za ku ɗauki farantai,
Do this: take censers for yourselves—Korah and all his company—
7 ku zuba wuta a ciki, ku kuma zuba musu turaren wuta a gaban Ubangiji. Sa’an nan wanda Ubangiji ya zaɓa a tsakaninmu sh ne mai tsarki. Ku Lawiyawa ku ne kuka wuce gona da iri!”
and put fire in them and put incense on them before YHWH tomorrow, and it has been, the man whom YHWH chooses, he [is] the holy one—enough of you, sons of Levi!”
8 Musa ya kuma ce wa Kora, “Yanzu ku saurara, ku Lawiyawa!
And Moses says to Korah, “Now hear, sons of Levi;
9 Ashe, bai ishe ku ba, cewa Allah na Isra’ila, ya keɓe ku daga sauran jama’ar Isra’ilawa, ya kuma kawo ku kusa da shi don ku yi aiki a tabanakul na Ubangiji, ku kuma tsaya a gaba jama’a don ku yi musu aiki?
is it little to you that the God of Israel has separated you from the congregation of Israel to bring you near to Himself, to do the service of the Dwelling Place of YHWH, and to stand before the congregation to serve them?
10 Ya kawo ku da kuma dukan’yan’uwanku Lawiyawa kusa da shi, amma yanzu kuna ƙoƙari ku karɓi aikin firist.
Indeed, He brings you near, and all your brothers, the sons of Levi, with you—and you have also sought the priesthood!
11 Kai da ƙungiyarka kun haɗa kai kuna yi wa Haruna gunaguni, amma wane ne Haruna? A zahiri tawaye ne kuke wa Ubangiji.”
Therefore, you and all your congregation are meeting against YHWH; and Aaron, what [is] he, that you murmur against him?”
12 Sai Musa ya aika a kira Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab maza, amma suka ce, “Ba za mu zo ba!
And Moses sends to call for Dathan and for Abiram, sons of Eliab, and they say, “We do not come up!
13 Bai isa ba ne da ka fitar da mu daga ƙasar mai zub da madara da zuma, ka kawo mu nan hamada don ka kashe mu? Yanzu kuma so kake ka mai da kanka sarki a bisanmu?
Is it little that you have brought us up out of a land flowing with milk and honey, to put us to death in a wilderness, that you also certainly make yourself prince over us?
14 Ban da haka ma, ai, ba ka riga ka kai mu ƙasar mai zub da madara da zuma ba, ba ka ba mu gādon filaye da gonakin annabi ba, yanzu kuma kana so ka ruɗe mu. Mun ƙi, ba za mun zo ba!”
Indeed, you have not brought us into a land flowing with milk and honey, nor do you give an inheritance of field and vineyard to us; do you pick out the eyes of these men? We do not come up!”
15 Sai Musa ya husata ƙwarai, ya ce wa Ubangiji, “Kada ka karɓi hadayarsu. Ban ƙwace wani jakinsu ba, ban kuwa cuce waninsu ba.”
And it is very displeasing to Moses, and he says to YHWH, “Do not turn to their present; I have not taken one donkey from them, nor have I afflicted one of them.”
16 Musa ya ce wa Kora, “Da kai da kuma dukan ƙungiyarka za ku bayyana a gaban Ubangiji gobe, kai da su. Haruna ma zai kasance a can.
And Moses says to Korah, “You and all your congregation, be [present] before YHWH—you, and they, and Aaron—tomorrow;
17 Kowannenku zai ɗauki faranti yă zuba turare a ciki. Wato, farantai 250 ke nan, a kuma miƙa su a gaban Ubangiji. Kai da Haruna za ku miƙa farantanku, ku ma.”
and let each take his censer and you have put incense on them, and each has brought his censer near before YHWH—two hundred and fifty censers; indeed, you and Aaron, each [with] his censer.”
18 Sai kowane mutum ya ɗauki farantinsa, ya sa wuta da kuma turare a ciki, suka tsaya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada.
And they each take his censer, and put fire on them, and lay incense on them, and they stand at the opening of the Tent of Meeting with Moses and Aaron.
19 Sa’ad da Kora ya tara mabiyansa don su yi hamayya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan taron.
And Korah assembles all the congregation against them at the opening of the Tent of Meeting, and the glory of YHWH is seen by all the congregation.
20 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And YHWH speaks to Moses and to Aaron, saying,
21 “Ku ware kanku daga taron nan don in gama da su nan take.”
“Be separated from the midst of this congregation, and I consume them in a moment”;
22 Amma Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki suka tā da murya suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin dukan’yan adam, za ka husata da dukan taron ne, bayan mutum ɗaya ne ya yi zunubi?”
and they fall on their faces, and say, “God, God of the spirits of all flesh—one man sins, and are You angry against all the congregation?”
23 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
And YHWH speaks to Moses, saying,
24 “Faɗa wa taron cewa, ‘Ku nisanci tentin Kora, da na Datan, da na Abiram.’”
“Speak to the congregation, saying, Go up from around the dwelling place of Korah, Dathan, and Abiram.”
25 Musa ya tashi ya tafi wurin Datan da Abiram, dattawan Isra’ilawa kuwa suka bi shi.
And Moses rises, and goes to Dathan and Abiram, and [the] elderly of Israel go after him,
26 Ya gargaɗe taron ya ce, “Ku ƙaurace wa tentin waɗannan mugayen mutane! Kada ku taɓa kome da yake nasu, domin kada a shafe ku saboda zunubansu.”
and he speaks to the congregation, saying, “Now turn aside from the tents of these wicked men, and do not come against anything that they have, lest you are consumed in all their sins.”
27 Sai suka tashi daga inda tentin Kora, da Datan, da Abiram suke. Datan da Abiram kuwa suka fita suna tsaye tare da matansu da’ya’yansu da’yan ƙananansu a ƙofar tentinsu.
And they go up from the dwelling place of Korah, Dathan, and Abiram, from all around, and Dathan and Abiram have come out, standing at the opening of their tents, with their wives, and their sons, and their infants.
28 Sai Musa ya ce musu, “Da haka za ku san cewa Ubangiji ne ya aiko ni, in yi dukan waɗannan abubuwa, ba da nufin kaina na yi su ba.
And Moses says, “By this you know that YHWH has sent me to do all these works, that [they are] not from my own heart;
29 In waɗannan mutane sun mutu kamar yadda mutane suke mutuwa, in abin da yakan sami kowa shi ne ya same su, to, ba Ubangiji ne ya aiko ni ba.
if these die according to the death of all men, or the charge of all men is charged on them, YHWH has not sent me;
30 Amma in Ubangiji ya kawo wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara cikin kabari a raye, ta haka za ku sani mutanen nan sun rena Ubangiji.” (Sheol h7585)
but if YHWH does a strange thing, and the ground has opened her mouth and swallowed them and all that they have, and they have gone down alive to Sheol, then you have known that these men have despised YHWH.” (Sheol h7585)
31 Nan da nan da ya gama faɗi wannan, sai ƙasa ta tsage inda Datan da Abiram suke tsaye,
And it comes to pass at his finishing speaking all these words, that the ground which [is] under them cleaves,
32 ta kuma buɗe bakinta, ta haɗiye su tare da mutanen gidansu da dukan mutanen Kora da dukan abin da yake mallakarsu.
and the earth opens her mouth and swallows them, and their houses, and all the men who [are] for Korah, and all the goods,
33 Suka gangara cikin kabari da rai, tare dukan mallakarsu; ƙasa ta rufe su, suka hallaka, suka rabu da jama’ar. (Sheol h7585)
and they go down—they and all that they have—alive to Sheol, and the earth closes over them, and they perish from the midst of the assembly; (Sheol h7585)
34 Da jin kukansu, dukan Isra’ilawa da suke kewaye da su suka gudu, suna ihu, “Ƙasa za tă haɗiye mu, mu ma!”
and all Israel who [are] around them have fled at their voice, for they said, “Lest the earth swallow us”;
35 Sai wuta ta fito daga wurin Ubangiji ta cinye mutane 250 da suke miƙa hadaya da turare.
and fire has come out from YHWH and consumes the two hundred and fifty men bringing the incense near.
36 Ubangiji ya ce wa Musa,
And YHWH speaks to Moses, saying,
37 “Ka gaya wa Eleyazar ɗan Haruna, firist, yă kawar da farantan ƙona turare daga wurin da wutar ta cinye, yă watsar da gawayin a wani wuri, gama farantan tsarkakakku ne,
“Say to Eleazar son of Aaron the priest to lift up the censers from the midst of the burning and scatter the fire away, for they have been hallowed.
38 gama an yi amfani da farantan don miƙa mini turare. Sai ka ɗauki farantan mutanen da suka yi zunubin da ya jawo musu mutuwa ka ƙera farantan, ka yi murfin bagade da su, gama an miƙa su a gaban Ubangiji, suka zama tsarkakakku. Bari su zama alama ga Isra’ilawa.”
[As for] the censers of these sinners against their own souls, indeed, they have made them [into] spread-out plates [for] a covering for the altar, for they have brought them near before YHWH, and they are hallowed; and they become a sign to the sons of Israel.”
39 Haka Eleyazar, firist, ya tattara farantan tagulla waɗanda mutanen da aka hallaka suka kawo, ya ƙera murfin bagade da su,
And Eleazar the priest takes the bronze censers which they who are burned had brought near, and they spread them out [for] a covering for the altar—
40 yadda Ubangiji ya umarce shi, ta wurin Musa. Wannan ya zama abin tuni ga Isra’ilawa domin kada wani da ba firist ba, bai kuwa fito a cikin zuriyar Haruna ba, yă zo don yă ƙona turare a gaban Ubangiji, domin kada yă zama kamar Kora da mabiyansa.
a memorial to the sons of Israel, so that a stranger who is not of the seed of Aaron does not draw near to make incense before YHWH, and is not as Korah and as his congregation, as YHWH has spoken by the hand of Moses to him.
41 Kashegari dukan taron Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna suka ce, “Kun kashe mutanen Ubangiji.”
And on the next day all the congregation of the sons of Israel murmurs against Moses and against Aaron, saying, “You have put the people of YHWH to death.”
42 Bayan haka, sai dukan jama’a suka taru domin su nuna rashin yardansu da abin da suke zato Musa da Haruna ne suka aikata. Da suka fuskanci Tentin Sujada, nan take sai girgije ya rufe shi, ɗaukaka Ubangiji kuwa ta bayyana.
And it comes to pass, in the congregation being assembled against Moses and against Aaron, that they turn toward the Tent of Meeting, and behold, the cloud has covered it and the glory of YHWH is seen;
43 Sai Musa da Haruna suka je gaban Tentin Sujada,
and Moses comes—Aaron also—to the front of the Tent of Meeting.
44 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,
And YHWH speaks to Moses, saying,
45 “Ku nisanci wannan taro, gama yanzu nan zan hallaka su.” Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki.
“Get up from the midst of this congregation, and I consume them in a moment”; and they fall on their faces,
46 Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki farantinka ka sa turare a ciki, da wuta daga bagade, ka yi maza ka tafi wajen taron, ka yi kafara dominsu. Gama fushin Ubangiji ya riga ya sauko; an kuma fara annoba.”
and Moses says to Aaron, “Take the censer and put fire on it from off the altar, and place incense, and go quickly to the congregation and make atonement for them, for the wrath has gone out from the presence of YHWH—the plague has begun.”
47 Saboda haka Haruna ya yi kamar yadda Musa ya faɗa, ya ruga a guje zuwa tsakiyar taron. An riga an fara annobar a cikin mutane, amma Haruna ya miƙa turaren ya kuma yi kafara dominsu.
And Aaron takes [it] as Moses has spoken, and runs to the midst of the assembly, and behold, the plague has begun among the people; and he gives the incense, and makes atonement for the people,
48 Ya tsaya tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya.
and stands between the dead and the living, and the plague is restrained;
49 Amma mutane 14,700 ne suka mutu a annobar, ban da waɗanda suka mutu a sanadin Kora.
and those who die by the plague are fourteen thousand and seven hundred, apart from those who die for the matter of Korah;
50 Sai Haruna ya komo wurin Musa a ƙofar Tentin Sujada, gama annobar ta ƙare.
and Aaron turns back to Moses, to the opening of the Tent of Meeting, and the plague has been restrained.

< Ƙidaya 16 >